Yara Kusan Miliyan 3 Za A Yiwa Rigakafin Cutukan Polio Da Kyanda A Jihar Sakkwato
Published: 7th, October 2025 GMT
An yi wa yara miliyan biyu da dubu takwas allura, yayin aikin rigakafin cutar Polio, kyanda, da kuma Gaida a jihar Sakkwato.
Gwamna Ahmed Aliyu Sokoto ya bayyana haka a wajen kaddamar da shirin da aka gudanar a garin Bodinga da ke karamar hukumar Bodinga.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan hulda da manema labarai na ofishin mataimakin gwamnan jihar, Garba Muhammed, Alhaji Ahmed Aliyu ya raba wa manema labarai, ya bayyana cewa aikin polio din zai gudana ne a daukacin unguwanni 244 dake fadin jihar.
Don haka ya yi kira ga shugabannin al’umma da na addini da kuma abokan ci gaba da masu ruwa da tsaki da su ba da himma wajen tallafa wa wannan aikin ta hanyar hada kai da kuma tabbatar da cewa duk yaran da suka cancanta sun samu alluran rigakafin da ake bukata.
A cewar sa, za a yi allurar rigakafin ga yara ‘yan watanni 9 zuwa 14, kuma za a kwashe kwanaki 10 ana yin wannan aikin.
Ya bayyana cewa Najeriya ce tafi kowacce kasa yawan yara masu kamuwa da cutar kyanda da gaida a duniya.
Ya kara da cewa lamarin ya nuna akwai gagarumin gibi a fannin rigakafi na yaran da ba sa karbar alluran rigakafin a daidai lokacin da ya kamata, wanda ke haifar da munanan sakamako kamar kuramta, makanta, da sauran matsaloli.
Gwamnan wanda mataimakin gwamnan jihar Alhaji Idris Mohammed Gobir ya wakilta, ya jaddada aniyar gwamnatinsa na gina tsarin kiwon lafiya wanda ba wai kawai ake iya samunsa ba, har ma da samar da ingantacciyar kulawa da tallafawa gano cututtuka da wuri.
A nasa jawabin kwamishinan lafiya na jihar Dr. Faruk Umar Abubakar Wurno ya bayyana cewa an samar da rukunin ma’aikata da zasu ziyarci unguwanni 244, inda kowane rukunin ma’aikatan akwai mutum 11 a cikin su.
Dakta Faruk Umar Wurno ya kara da cewa, jihar ta samu alluran rigakafi guda 3,072,520 daga hukumar kula da lafiya matakin farko ta kasa.
Kwamishinan ya kuma yi amfani da damar wajen mika godiyarsa ga gwamnatin jihar bisa bada tallafin da takwarorinta ke yi na wannan aikin.
Da yake tsokaci, wakilin mai alfarma Sarkin Musulmi kuma Hakimin Wurno, Alhaji Kabir Alhassan Cigari, ya bayar da tabbacin cewa sarakunan sun jajirce wajen ganin an cimma nasarar shirin.
MUSTAPHA/Sakkwato
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kyanda
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
Ministar wadda ta je kamfanin domin daukar sabuwar motarta ta alfarma kirar Nord Demir SUB da kamfanin ya hada nataimakin Shugaban jami’ar na sashen kula da ilimi da gudanar da bincike Farfesa Bola Oboh da kuma Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi ne, suka karbi bakuncinta.
A jawabin da ta gabatar a lokacin ziyarar ministar ta bayyana cewa,Duba da yarjejeniyar hada-hadar kasuwanci wajen fitar da kaya zuwa ketare kamfanin zai iya yin amfani da wannan samar waken fitar da motocinsa zuwa ketare.
Ta kara da cewa, Nijeriya na da gurare biyu ne da ake hada motoci da suka hada da, na wannan jami’ar da kuma na EPs, inda ta yi nuni da cewa, karfin da kamfanin ya ke da shi, zai iya cike gibin bukatar da ake da ita, ta ‘yan kasar na bukatar motocin.
Ya ci gaba da cewa, za mu ci gaba da kara karfafa kwarin guwair ‘yan kasar domin da kuma sauran kamfanoni masu zaman kansu domin su rinka sayen kayan da kamfanonin kasar, suka sarrafa da kuma hada su.
Ta ce, wannan babban abin alhari ne, ganin cewa, a wannan jami’ar ce, aka hada wannan mortar.
Shi kuwa a na sa jawabin Farfesa Oboh ya bayyana cewa, muna Myrna da wannan shirin na Gwamnatin Tarayya wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ke jagorantar bai wa ‘yan kasar kwarin guwair sayen kayan da aka sarrafa a cikin kasar
A cewarsa, jami’ar ta UNILAG, ba wai kawai na yin alfahari da samun wannan wajen hada motocin ba ne, kadai amma ta na alharin da cewa, an samar da wajen a jami’ar.
Shi ma, Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi, a yayin da ya ke nuna jin dadinsa kan gudunmwar da ministar ke bai wa kamfanin ya a bayyana cewa, na yi matukar farin ciki ganin cewa, ministar ta kasance daya daga cikin abokan cinikayyar mu
Kazalika, Shugaban ya kuma gode wa mahukunta jami’ar ta UNILAG kan yin hadaka da kamfanin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA