Aminiya:
2025-10-13@15:47:19 GMT

Tinubu ya umarci NAHCON ta ƙara rage kuɗin aikin Hajjin 2026

Published: 7th, October 2025 GMT

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta sake rage kuɗin aikin Hajjin shekarar 2026 nan take, kuma ta fitar da sabon farashin cikin kwana biyu.

Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan hukumar ta sanar da rafin kimanin N200,000 a kan farashin da maniyyata suka biya a bara.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ne ya isar da umarnin shugaban kasa yayin wani taro da ya yi da shugabanni da mambobin hukumar NAHCON a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, a ranar Litinin.

Shettima ya buƙaci a samu hadin kai tsakanin jami’an jihohi da na tarayya, ciki har da gwamnoni, wajen fitar sabon farashin da ya dace da yanayin tattalin arzikin ƙasar.

An fara bincikar Ganduje kan zargin karkatar da N4bn BBNaija S10: Ban san yadda zan kashe N150m da na lashe ba — Imisi Eniola

Ya kuma bukaci masu ruwa da tsaki su gaggauta biyan kuɗaɗen da suka dace zuwa Babban Bankin Najeriya (CBN) domin tabbatar da cika tsare-tsare da kuma gudanar da aikin Hajjin cikin lumana.

Da yake magana da manema labarai bayan taron, Mataimakin Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Sanata Ibrahim Hadejia, ya ce an gudanar da taron ne domin kammala shirye-shiryen aikin Hajjin 2026, musamman batun farashin kujera.

Ya ce manufar gwamnati ita ce rage wa maniyyata kuɗin tafiya, la’akari da sauye-sauyen tattalin arzikin da ake aiwatarwa a yanzu.

Hadejia ya ce, “Tattalin arziki yana ƙara samun daidaito, kuma darajar naira tana ƙaruwa sakamakon gyare-gyaren da gwamnati ke yi. Idan maniyyata sun biya tsakanin Naira miliyan 8.5 zuwa 8.6 a bara saboda tsadar Dala, yanzu da naira ta ƙara daraja, ya kamata a rage farashin.”

Ya ce an umarci NAHCON ta yi amfani da ainihin farashin canji na yanzu, yana mai cewa idan hakan ta tabbata, za a samu gagarumin sauƙin kuɗin aikin Hajji.

Shi ma Sakatare na NAHCON, Dakta Mustapha Mohammad, ya ce wannan umarni na shugaban ƙasa zai ƙara yawan maniyyata aikin Hajjin bana.

“Wannan ci gaba ne mai kyau. Rage kuɗin zai taimaka wa Musulmi da dama su samu damar yin wannan rukuni na addini. Za mu yi aiki tuƙuru tsakanin yau da gobe domin rage kuɗin zuwa matakin da kowa zai iya biya,” in ji shi.

A nasa bangaren, Shugaban Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi kuma Mataimakin Shugaban Ƙungiyar shugabannin Hukumomin Alhazai na jihohi da Abuja, Alhaji Faruk Aliyu Yaro, ya bayyana farin cikinsa da umarnin shugaban ƙasa.

“Mun yi matuƙar farin ciki da wannan mataki na shugaban ƙasa da mataimakinsa. Wannan zai taimaka wajen rage kuɗin aikin Hajji, kuma muna gode wa Allah da gwamnati,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: maniyyata rage kuɗin

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

Ministar wadda ta je kamfanin domin daukar sabuwar motarta ta alfarma kirar Nord Demir SUB da kamfanin ya hada nataimakin Shugaban jami’ar na sashen kula da ilimi da gudanar da bincike Farfesa Bola Oboh da kuma Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi ne, suka karbi bakuncinta.

 

A jawabin da ta gabatar a lokacin ziyarar ministar ta bayyana cewa,Duba da yarjejeniyar hada-hadar kasuwanci wajen fitar da kaya zuwa ketare kamfanin zai iya yin amfani da wannan samar waken fitar da motocinsa zuwa ketare.

 

Ta kara da cewa, Nijeriya na da gurare biyu ne da ake hada motoci da suka hada da, na wannan jami’ar da kuma na EPs, inda ta yi nuni da cewa, karfin da kamfanin ya ke da shi, zai iya cike gibin bukatar da ake da ita, ta ‘yan kasar na bukatar motocin.

 

Ya ci gaba da cewa, za mu ci gaba da kara karfafa kwarin guwair ‘yan kasar domin da kuma sauran kamfanoni masu zaman kansu domin su rinka sayen kayan da kamfanonin kasar, suka sarrafa da kuma hada su.

 

Ta ce, wannan babban abin alhari ne, ganin cewa, a wannan jami’ar ce, aka hada wannan mortar.

 

Shi kuwa a na sa jawabin Farfesa Oboh ya bayyana cewa, muna Myrna da wannan shirin na Gwamnatin Tarayya wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ke jagorantar bai wa ‘yan kasar kwarin guwair sayen kayan da aka sarrafa a cikin kasar

A cewarsa, jami’ar ta UNILAG, ba wai kawai na yin alfahari da samun wannan wajen hada motocin ba ne, kadai amma ta na alharin da cewa, an samar da wajen a jami’ar.

Shi ma, Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi, a yayin da ya ke nuna jin dadinsa kan gudunmwar da ministar ke bai wa kamfanin ya a bayyana cewa, na yi matukar farin ciki ganin cewa, ministar ta kasance daya daga cikin abokan cinikayyar mu

Kazalika, Shugaban ya kuma gode wa mahukunta jami’ar ta UNILAG kan yin hadaka da kamfanin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tattalin Arziki Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho October 10, 2025 Tattalin Arziki An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi  October 10, 2025 Tattalin Arziki Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya