Aminiya:
2025-11-27@22:29:53 GMT

A ba mu damar ɗaukar makamai don kare kanmu daga ’yan bindiga —Sakkwatawa

Published: 7th, October 2025 GMT

Al’ummar Ƙaramar Hukumar Kebbe da ke Jihar Sakkwato sun roƙi gwamnati ta ba su dama su riƙa ɗaukar makamai domin kare kansu daga hare-haren ’yan bindiga da suka addabi yankinsu.

Mutanen sun ce sun gaji da kashe-kashe, sace-sace, da kona gidaje da gonakinsu da ’yan bindiga ke yi, wanda ke jefa su cikin tsananin wahala da asara.

Mazauna yankin sun ce daga cikin garuruwa 17 da ke cikin Ƙaramar Hukumar Kebbe, an riga an raba mazauna akalla 11 da gidajensu saboda yawan hare-hare.

Wani shugaban al’umma a yankin, Tukur Muhammad Fakum, ya shaida wa BBC cewa halin da suke ciki ya sa suka fara tunanin yadda za su kare kansu da kansu.

Ya kamata a karɓe ikon naɗa Shugaban INEC daga hannun Shugaban ƙasa — IPAC  Jerin ministocin da zargin takardun bogi ya tabaibaye su

“Yanzu muna tattaunawa. Waɗanda ke da ƙanana gonaki sun riga sun sayar, haka ma waɗanda ke da ƙananan gidaje. Idan muka iya siyan bindiga, za mu bai wa matasanmu su kare mu,” in ji shi.

Ya ce: “Gwamnati ce ya kamata ta kare mu, amma idan ba za ta iya ba, to ta bar mu mu mallaki makamai don matasanmu su kare rayukansu da garuruwansu.”

Fakum ya ƙara da cewa halin da ake ciki ya durƙusa da tattalin arzikin yankin gaba ɗaya.

“Babu abinci. Mutane da ba su taɓa kwana a masallaci ba yanzu suna kwana a can. Ka farka a yau, ka gudu zuwa wani wuri da ba ka taɓa zuwa ba, saboda neman tsira. Lamarin ya kai matuƙar muni,” in ji shi.

Ƙoƙarin da BBC ta yi na jin ta bakin jami’an gwamnati da hukumomin tsaro bai yi nasara ba, domin babu wanda ya amsa kira har zuwa lokacin da aka wallafa rahoton.

Jihar Sakkwato na daga cikin jihohin da suka fi fama da hare-haren ’yan bindiga a ’yan shekarun nan, musamman a ƙananan hukumomin Isa, Sabon Birni, da Kebbe.

Baya ga ’yan bindigar Bello Turji da ke da sansanoni a sassan jihar, mayaƙan Lakurawa sun ɓulla a yankin a ’yan baya-bayan nan.

Masana tsaro sun yi gargaɗi cewa ƙungiyar na iya zama sabon barazana ga jihar da ma yankin Arewa maso Yamma gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hare hare yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano

Rahotanni na cewa ’yan bindiga sun sace wasu mutum takwas a garin Biresawa da ke Karamar Hukumar Tsanyawa ta Jihar Kano a daren jiya na Litinin.

Wata majiyar da ta tabbatar da lamarin ta shaida wa Aminiya cewa maharan sun shiga garin tsakanin 11 na dare zuwa 12 na tsakar dare, inda suka yi awon gaba da maza biyu da mata shida.

’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai

Wani ɗan uwa ga waɗanda aka sace, Kabiru Usman, ya ce maharan sun zo ne a ƙafa ɗauke da makamai, suka kuma yi garkuwa da matarsa Umma, ɗiyarsa mai shekara 17, da matar ɗan’uwansa da wasu mata biyu daga Tsundu mai makwabtaka.

Ya ce al’ummar garin sun yi ƙoƙarin daƙile harin amma suka kasa saboda ƙarancin makamai, duk da cewa sun sanar da ’yan sanda da sojoji tun kafin faruwar harin bayan samun bayanan cewa ’yan bindigar na dosar yankin.

Ya roƙi gwamnati ta ɗauki mataki wajen ceto mutanen da aka sace da kuma kare rayukan mazauna yankin.

Aminiya ta yi ƙoƙarin ji ta bakin Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa, sai da har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia
  • An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano