Ya kamata a karɓe ikon naɗa Shugaban INEC daga hannun Shugaban ƙasa — IPAC
Published: 7th, October 2025 GMT
Ƙungiyar shugabannin jam’iyyun siyasa (IPAC) ta ce lokaci ya yi da za a cire ikon naɗa shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) daga hannun Shugaban ƙasa.
Ƙungiyar ta ce kamata ya yi a kafa wani kwamiti mai zaman kansa da zai riƙa yin naɗin shugaban INEC da kwamishinoni da sakatare na hukumar domin tabbatar da gaskiya da cin gashin kai na hukumar.
Shugaban ƙungiyar IPAC, Dakta Yusuf Mamman Ɗantalle, ne ya bayyana haka a wani taro da suka yi da kwamitin Majalisar Wakilai da ke nazarin kundin tsarin mulki a Abuja.
Ya ce tsarin da ake amfani da shi yanzu na bai wa shugaban ƙasa damar zaɓar shugaban INEC na iya rage amincewar jama’a da hukumar.
Jerin ministocin da zargin takardun bogi ya tabaibaye su Tinubu ya umarci NAHCON ta rage kuɗin aikin Hajjin 2026“Don a tabbatar da sahihancin hukumar, dole a cire wannan iko daga hannun shugaban ƙasa. A kafa kwamiti da zai haɗa jam’iyyun siyasa, ƙungiyoyin farar hula, Lauyoyi, da wakilan Majalisar Dokoki domin su zaɓi shugaban INEC,” in ji shi.
Ɗantalle ya ce hakan zai taimaka wajen tabbatar da adalci da gaskiya a cikin zaɓe, musamman duba da yadda aka yi ta samun ƙorafe-ƙorafe kan yadda zaɓukan baya suka gudana.
Wannan ra’ayi na IPAC ya yi daidai da irin shawarar da tsoffin shugabanni irin su Olusegun Obasanjo da Goodluck Jonathan suka taɓa bayarwa, inda suka nemi a inganta tsarin naɗin shugaban hukumar domin ƙara sahihancin zaɓe.
A cewar su, wannan gyara zai taimaka wajen dawo da amincewar jama’a da tsarin dimokuraɗiyya, musamman kafin zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.
A yanzu haka wa’adin shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, na dab da ƙarewa bayan ya jagoranci zaɓukan 2019 da na 2023. Tuni aka fara raɗe-raɗin wanda zai maye gurbinsa.
Wasu jam’iyyun kuma sun bayar da shawarar cewa jam’iyyun da ke da wakilai a Majalisar Dokoki ta Ƙasa ne kawai za su riƙa bayar da sunayen wanda za a zaɓa domin wannan muƙami.
A nata ɓangaren, Ƙungiyar matasa Musulmi ta Lasa (NMYA) ta nemi majalisa ta duba kudirin doka da ke neman cire ikon shugaba da gwamnonin jihohi wajen naɗin shugabannin INEC da na hukumomin zabe na jihohi (SIECs).
Shugaban ƙungiyar, Injiniya Abdulraham Aliyu, ya ce, “Zaɓe mai gaskiya ba zai tabbata ba muddin shugaba yana da ikon naɗa wanda zai kula da shi.”
Ya ƙara da cewa fasahohin zamani kamar BVAS da IReV da INEC take amfani da su wajen gudanar da zaɓe ba za su yi tasiri ba idan hukumar ba ta zama mai gaskiya ba.
A gefe guda, ƙungiyar CISLAC ta nuna goyon bayanta ga kafa tsarin nadin INEC mai zaman kansa, amma ta ce ba ta goyi bayan rushe hukumomin zaɓe na jihohi ba, saboda hakan zai rage ƙarfin tsarin tarayya.
A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, wanda shi ne shugaban kwamitin gyaran kundin tsarin mulki, ya ce, “Gyaran kundin tsarin mulkin da ake yi yanzu dole ne ya haifar da dimokuraɗiyya mai ɗorewa, inda jam’iyyun siyasa za su samu daidaito.”
Shi ma Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, wanda Sanata Mohammed Tahir Monguno ya wakilta, ya ce zaɓe mai gaskiya da ’yancin ƙananan hukumomi su ne tushen amincewar jama’a da gwamnati.
Ya ƙara da cewa goyon bayan kafa ’yan sanda na jihohi na iya zama hanyar magance matsalar tsaro a ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ikon naɗa Shugaban INEC Shugaban Ƙasa Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
Larijani Iran Tana Maraba Da Tattaunawa Ta Gaskiya Amma Ba Tsararren Sakamako Ba
Babban sakataren tsaron kasar Iran Dr Ali Larijani a shafinsa na X ya soki siyasar Amurka a lokacin ziyararsa a kasar Pakistan kuma ya jaddada cewa Tehran tana son ayi gaskiya a duk tattaunawa da za’a yi.
Kalaman na larijani yana nuna matsayar iran ne kan diplomasiyar iyakoki, yace yanci da mallaka wasu abubuwa ne da babu sulhu a kansu, don haka duk wata tattaunawa da Amurka dole ne ta zama cikin yanci da daidaito, za’a iya tattaunawa amma ta gudana ba tare da nuna fifiko ba.
Amurka tana kokarin nuna kanta a matsayin wadda za ta kawo sauyi a kowanne lamari na duniya, amma wannan wani nau’i ne na yaudarar kai, don haka mun yarda da tattaunawa ta gaskiya ba ta wucin gadi ba, kuma dole ne a kayyade sakamakon kowacce tattaunawa.
Rashin yarda ce ta sa tattaunawa tsakanin Amurka da iran ta samu cikas a baya, jamai’an kasar Iran na jaddadawa kan wuraren da Amurka tayi Amfani da matsin lamba ko kuma daukar matakin soji wanda hakan ke kara sa shakkun Tehran game da manufofin Amurka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka November 26, 2025 Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza November 26, 2025 Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe November 26, 2025 Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta November 26, 2025 Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki November 26, 2025 Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin November 26, 2025 Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah November 26, 2025 UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin Lebanon November 26, 2025 Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci