Leadership News Hausa:
2025-10-13@15:47:29 GMT

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Published: 4th, October 2025 GMT

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Rushewar wannan gada na haifar mana da matsala sosai. Gwamnati ta taimaka ta gyara,” in ji Wayu Bamga, mazaunin yankin.

Nanlong Nyas ya ƙara da cewa, “Gyaran da aka yi bai daɗe ba kafin ruwa ya sake lalata gadar.

Wasu direbobi kamar Umar Sa’adu da Abubakar Haruna sun ce duk lokacin da suka isa wurin gadar, sai sun biya ma’aikata su tura motarsu kafin su iya tsallaka rafi kana su ci gaba da tafiya.

Rushewar Gadar Namne Ta Taraba Ta Tsayar Da Zirga-Zirga

A Jihar Taraba kuwa, Gadar Namne dake kan hanyar Jalingo–Wukari  ta rushe a watan Agustan 2024 bayan ruwan sama mai yawa, kuma har yanzu shekara guda bayan haka, babu wani gyara da gwamnatin tarayya ko ta jiha ta fara.

Gadar tana da muhimmanci sosai saboda tana haɗa Arewa maso Gabas da Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma da kuma babban birnin Tarayya (Abuja). Duk da alƙawarin da Gwamna Agbu Kefas, da gwamnatin tarayya da hukumar ci gaban Arewa Maso Gabas (North-East Development Commission (NEDC) suka yi, babu wani aikin gyara da aka fara har yanzu.

A yanzu, matafiya suna amfani da kwale-kwale wajen tsallaka kogin, yayin da ƙananan motoci da babura ne kawai ke iya bin hanyar. Ana kuma cajin matafiya kuɗi don tsallaka kogin.

Farashin sufuri da kayan masarufi sun tashi saboda doguwar hanya da direbobi ke bi,” in ji wani mazaunin yankin. “Tsallaka rafi da kwale-kwalen  kuma na da hatsari, musamman ga waɗanda ba su saba ba.”

Tasirin A ƙasa baki ɗaya

A wasu jihohi kamar Kebbi, da Kogi da Neja, irin wannan ambaliya ta lalata gadoji da hanyoyi, ta katse alaƙa tsakanin ƙauyuka da birane, ta kuma jawo cikas ga harkokin kasuwanci da tattalin arziƙi.

Masana harkokin gine-gine da muhalli sun yi gargaɗi cewa, sai an samar da tsarin ƙasa baki ɗaya na magance ambaliya da kuma yin gadaje da hanyoyi masu jure ruwa, idan ba haka ba, za a ci gaba da fuskantar irin wannan ɓarnar kowace shekara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ambaliya Kwara Ruwa Ruwan Sama

এছাড়াও পড়ুন:

Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola

 

Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya (NFF) ta tabbatar da cewa ta dauki matakin gaggawa bayan faruwar lamarin inda aka aike da wani jirgin sama daga Legas domin jigilar tawagar zuwa Uyo, sai dai lamarin ya haifar da tsaiko a shirin da tawagar ta ke yi na tunkarar jamhuriyar Benin a wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya na shekarar 2026.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0 October 9, 2025 Wasanni Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane October 7, 2025 Wasanni Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni October 6, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanzu-Yanzu: ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki Na Tsawon Mako Biyu
  • Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi 
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida