Leadership News Hausa:
2025-11-27@21:15:35 GMT

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

Published: 4th, October 2025 GMT

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

Akwai amfani saboda watarana wani abu zai taso mai muhimmanci, iyayensa ba sa kusa za su saukaka ta hanyar kiransu. Matsalar sa lalacewar karatu, koyan dabi’un marasa kyau da masu kyau, basu ko siya musu ba laifi ba ne, amma dai a tsananta saka musu ido dan gudun baraka da lalacewa. Ya zamo kiran mai amfani ne da karatu za su rika yi da shi, ba tiktok ko Instagram ko Twitter ba.

Allah ka shirya mana zuriya, ka sa mu dace.

Sunana Anas Bin Malik Achilafiya, Karamar Hukumar ‘Yankwashi, Jihar Jigawa:

Amfanin bayar da waya ga kananan yara; yana saukaka musu sadarwa ga iyaye, abokai, da sauran su, samun ilimi da bincike ta hanyar intanet. Iya jawo jaraba, ko dogaro da waya. Zai iya bude kofa ga illolin yanar gizo (Shiga shafukan batsa, ko neman kudi ta hanyoyin da addini ya haramta), rage huldar mutum da mutane a zahiri. Shawara a kayyade lokacin amfani da waya, iyaye su saka idanu kan abin da yara ke amfani da shi. A sa hankali kan hadari da kuma amfani da ita wajen ilimi da sadarwa mai amfani.

Ubangiji Allah ka kara shirya mu, da zuri’armu shirin addinin musulunci. Allahumma Amin.

Sunana Aisha T. Bello, Jihar Kaduna:

Mahimmancin bawa yara waya shi ne; za su iya bincike kan abin da ya shafi karatunsu. Illar bawa yara masu karancin shekaru waya na da yawa; za su iya dauko dabi’u marasa kyau. Shawara yara su yi amfani da waya bisa jagorancin iyaye, waya ta zama hannun iyaye sai yara za su yi amfani da shi a basu kafin a sakar masu a hannunsu, a bari su iya bambancewa tsakanin tsaba da tsakuwa.

Sunana Muhammad Isah, Zareku Miga A Jihar Jigawa:

A gaskiya ni a nawa tunanin ba shi da wani amfani, hasali ma bata tarbiyya yake wajen bawa yara wayar hannu. A shawarance iyayen yara su kula sosai wajen basu wayar hannu, domin tana hana yara karatun addini dana zamani mai makon su mayar da hankali wajen karatu to, sai su buge da kallon finafinan hausa musamman ‘series film’.

Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor), Jihar Kano:

Babu wani alfanu, masu manyan shekaru ma ya ya aka cika bale yara ‘yan mitsitsina?, duk da wani lokacin sanda yaron zai dauki wayar baka sani ba sam, wasu kuma iyaye ne suke siyawa yaran wai gudun kar su taba musu tasu. Babban matsala ce duba da yadda zamani ya lalace lokacin da za a koyawa yaranka saka da mugun zare baka sani ba sai abin ya yi nisa, gyaruwarsa da wuya sai iyaye kuma a shiga wani hali. Babbar shawara a nan in ya zama dole sai yara sun rike waya, ita uwa sai ta kula sosai. Sannan in group ne na makaranta ta saka musu a tata wayar in wani aiki ne dai ta bada tata ayi kawai, Allah ya gyara mana yara ya kuma shirya mana su, Amin.

Sunana Abba Abubakar Yakubu, daga Jos, A Jihar Filato:

A fahimta ta inda illar take da tasiri shi ne bai wa yara babbar waya, don su rika aikin makaranta ko gogayya da sauran yaran manya. Iyaye masu arziki sun fi yin wannan kuskuren a wajen su hakan ba laifi ba ne, suna ganin hakan yana sa yara su saba da tafiya da zamani. Sai dai a ganina kuskure ne, yara su saba da amfani da babbar waya tun ba su gama balaga ba, kwakwalwar su ba ta kai yadda za su yi wa kansu tunani mai kyau ba. Sakamakon yadda wasu marasa tunani ke amfani da waya ko zaurukan sada zumunta da ake samu ta manyan wayoyi, suna tura abubuwan wadanda ka iya bata tarbiyyar yara. Amma ana iya ba su karamar waya da za su yi amfani da ita, don amsa kira.

Sunana Hafsat Sa’eed, Jihar Neja:

Akwai illah, babu illah. Illar ita ce, shige-shigen Tiktok, Instagram, da sauransu. Yara sun saba da kide-kiden shiga media suna ganin irin abubuwan da ake yi to, zuciya ba ta da kashi wani yaron yana iya zuwa ya ga abin da zai ga kamar burgewa ne, ya je ya fadawa kansa wani yanayi. Amfaninta kuma waya da ita ake harkokin ilimi, musamman idan yaro zai yi karatu wajen gogulin. Fatan mu shi ne Allah ya shirya mana yara.

Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Rano LGA, Jihar Kano:

Gaskiya a nawa fahimtar ba shi da amfani, idan ma akwai amfanin bai fi 2% cikin dari ba, in har ya kai kenan. Saboda ba ma iya yara ba, yanzu har da manya waya tana taka rawa sosai wajen koyar da yadda ake aikata wasu miyagun ayyukan, da kuma haddasa karairayi da gurbata tarbiyya da sauransu. Shawarata, idan ma ta kama ana bawa ire-iren wadannan yaran waya to, ya zamana akwai takaitaccen lokaci wanda za a rika karbe wannan wayar. Sannan kuma iyaye su rika binciken wayar, su wa wadannan yaran suke mu’amala da su da kuma me da me suke yi..

Sunana Zulaihat Adamu, Jihar Kaduna:

Gaskiya babu wata matsalar bayar wa, matsalolin basu taka kara sun karya ba. Saboda yanzu komai ya koma amfani da na’ura don cigaban al’umma, malamai da wasu makarantun suka mayar da aikinsu kan waya dan saukakawa. Shawara, shi yaron ya san dan me aka bashi wayar da kuma amfaninta a gurin shi, da tsara lokutan amfani da wayar a gareshi, dan yawan amfani da wayar ka’iya kashe idanuwa cikin sauki, kada a zo garin neman gira a rasa ido.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Wayar amfani da waya

এছাড়াও পড়ুন:

Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja

Wata tankar mai ta yi gobara a wani gudan mai a yankin Tungan-Bunu da ke Ƙaramar Hukumar Rijau a Jihar Neja, lamarin da ya janyo ƙonewar gidaje da kadarori da masu yawa.

Shaidu sun ce gobarar ta tashi ne a lokacin da tankar take shirin sauke mai a ranar Litinin da yamma, inda wutar ta bazu zuwa gidajen da ke kusa.

Duk da cewa babu wanda ya rasa ransa, lamarin ya haifar da firgici inda mazauna yankin suka yi ta tserewa suka bar gidajensu yayin da tankar ke ci da wuta.

Tankar mai ta yi hatsari a hanyar Lapai-Agaie Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno

A wani lamari ba daban, wata tankar mai ta kife a kan hanyar Lapai zuwa Agaie, lamarin da ya toshe hanya tare da haddasa cunkoson ababen hawa.

Shaidu sun ce tankar, wadda ke ɗauke da fetur daga Legas zuwa Gombe, ta kife ne da misalin karfe 10 na safe a ranar Litinin bayan jikinta ya rabu da kan motar, ya ƙetare hanya, abin da ya tayar da hankalin jama’a.

Wani mazaunin yankin, Malam Mahmud Abubakar, ya ce jami’an tsaro sun garzaya wajen domin tsare yankin, sannan aka tura ma’aikatan kashe gobara don kauce wa tashin wuta.

Ya ƙara da cewa lamarin ya faru ne a yankin Efu-Nda-Egbo na Ƙaramar Hukumar Lapai, inda ya haddasa cunkoson ababen hawa mai tsanani.

Kokarin tuntuɓar Darakta-Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, bai yi nasara ba, domin bai amsa kiran wayar da wakilinmu ya yi masa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja
  • Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi