Gwamnati Ta Sa Wutar Lantarki Ta Amfani Da Hasken Rana A Kasuwar Dutsen Jigawa
Published: 4th, October 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da aikin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana a Kasuwar Dutse Ultra-Modern Market, inda ya cika alkawarin gwamnatinsa na samar da tsaftataccen makamashi ga ‘yan kasuwa a jihar Jigawa.
Aikin wanda Hukumar Samar da Tattalin Arzikin Kasa da Samar da ayyukan yi ta Jihar Jigawa ta gudanar, ya hada shaguna 300 da wutar lantarki daga na’urorin hasken rana da aka sanya a cikin kasuwar, inda kowane shago kuma an saka masa fanka amfani da hasken rana kyauta.
Da yake jawabi a wajen bikin kaddamar da kasuwar a hukumance, Malam Umar Namadi ya ce shirin zai saukaka harkokin kasuwanci, da rage kashe kudi, da kuma bunkasa ribar ‘yan kasuwa.
Ya kuma yi alkawarin kafa fitilun masu amfani da hasken rana a kasuwar domin inganta tsaro, sannan ya bayyana wasu matakai na tallafa wa ‘yan kasuwa a jihar Jigawa, wadanda suka hada da samar da reshen bankin masana’antu (BOI) a jihar da kuma sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da bankin, inda gwamnatin jihar ta zuba naira biliyan 4 domin tallafa wa masu kananan sana’o’i.
Namadi ya kuma bukaci ’yan kasuwa a jihar da su yi amfani da wannan wurin su samu kudaden da kungiyar ta BOI ke da su don fadada kasuwancinsu.
A nasa jawabin shugaban kungiyar ‘yan kasuwa ta jihar Jigawa Alhaji Yahaya Ibrahim ya yabawa gwamnan bisa samar wa kasuwar wutar lantarki da hasken rana da kuma shirye-shiryen karfafawa ‘yan kasuwa daban-daban.
Ya kara da cewa aikin samar da wutar lantarkin kasuwar ya kasance farkon shirin Gwamna Namadi ga ‘yan kasuwa a jihar.
Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, wani bangare na aikin, na sanya na’urar samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana, mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ne ya kaddamar da shi a shekarar da ta gabata yayin wata ziyarar aiki da ya kai jihar, kuma a lokacin gwamnatin jihar ta yi alkawarin sa wutar a rumfuna kowa da kowa.
USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: lantarkin hasken rana amfani da hasken rana yan kasuwa a jihar da wutar lantarki a jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
Ya kara da cewa, ana ci gaba da kokari don ganin an iske masu yin kiwon shanu a kasar nan, domin fadakar da su kan muhimmancin rungumar wannan tsari na zamani.
Sai dai, ya yi nuni da cewa; wasu al’adu na haifar da tarnaki a tsakanin wasu masu kiwon a kasar na rungumar wannan tsarin.
“Na ga wasu gidajen gona da ake yin irin wannan dabara ta zamani, sannan kuma ana bayar da kulawar da ta kamata; wanda hakan ya sanya ake iya samar da litar madarar shanu daga tsakanin lita 15 zuwa 30,” in ji Jatau.
“Akwai wasu Fulani Makiyaya ‘yan kalilan da suka rungumi wannan tsari, misali a Jihar Bauchi; inda wani makiyayi ya rungumi wannan tsari tare kuma da amfanarsa yadda ya kamata,” a cewarsa.
“A lokacin da muka gudanar da ayyukanmu, wasu daga cikin Fulani Makiyaya, sun zo sun saurari wannan batu na dabara ta zamani tare da shanunsu, mun kuma aiwatar da tsarin a kan shanun nasu, inda daga baya suka ga yadda madarar shanunsu ta kara habaka,” in ji shi.
Jatau ya kara da cewa, suna kan ci gaba da bai wa Fulani Makiyaya kwarin guiwa, kan rungumar wannnan tsari, sai dai, wasu na fuskantar kalubale na kula da shanunsu da aka dora su a kan tsarin.
“A wasu kasashen na Afirka za ka cewa, Makiyayin da suka rungumi wannan tsari, na da shanu uku ne kacal da daukacin iyakansa suka dogara a kansu, wanda hakan ke ba su dama a kullam na samar da litar madara daga tsanakin 15 zuwa 20, “ a cewarsa.
Ya kara da cewa, hakan ya sanya a kullum suke samar wa da kansu dimbin riba, wanda kuma hakan ya sa ba su dogaro da aikin gwamnati ba kwata-kwata.
Ya yi nuni da cewa, idan har a raba daya za ka sayar da litar madara daya kan Naira 1,000, a wata za ka iya samun kudin shiga da suka kai Naira miliyan 1.8 da shanu uku kacal.
Ya ci gaba da cewa, da wannan ribar kadai za ka iya ci gaba da ciyar da shanun da lula da lafiyarsu da biyan ma’aikatan da ke kula da su da kuma daukar sauran dawainiyar kula da iyalanka.
Ya bayyana cewa, duba da cewa; ana fuskantar matsalar wajen da dabbobi za su yi kiwo a kasar nan, amma idan Fulani Makiyaya suka rungumi wannan tsari, hakan zai rage yawan samu rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani Makiyya a kasar.
Kazalika, ya sanar da cewa; idan masu kiwon suka dauki wannan tsari za a samu cewa, alfanun da za su samu ya dara irin na kiwon gargajiya da ake yi a cikin kasar.
Jatau ya bayyana cewa, wannan tsarin abu ne da ke da tsawon tarihi a kasar nan, domin an faro shi ne tun a shekarar 1949; tun bayan da aka dauki nau’in na jinsin daga wata gona da ke garin Shika a birnin Zaria, aka kuma kai shi zuwa cibiyar gudanar da bincike kan lafiyar dabbobi ta Bom.
Sai dai, ya bayyana cewa; rashin ci gaba da bibiyar wannan tsare-tsaren daga bangaren gwamnati, hakan ya haifar da koma baya ga wannan tsair.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA