Gwamnati Ta Sa Wutar Lantarki Ta Amfani Da Hasken Rana A Kasuwar Dutsen Jigawa
Published: 4th, October 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da aikin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana a Kasuwar Dutse Ultra-Modern Market, inda ya cika alkawarin gwamnatinsa na samar da tsaftataccen makamashi ga ‘yan kasuwa a jihar Jigawa.
Aikin wanda Hukumar Samar da Tattalin Arzikin Kasa da Samar da ayyukan yi ta Jihar Jigawa ta gudanar, ya hada shaguna 300 da wutar lantarki daga na’urorin hasken rana da aka sanya a cikin kasuwar, inda kowane shago kuma an saka masa fanka amfani da hasken rana kyauta.
Da yake jawabi a wajen bikin kaddamar da kasuwar a hukumance, Malam Umar Namadi ya ce shirin zai saukaka harkokin kasuwanci, da rage kashe kudi, da kuma bunkasa ribar ‘yan kasuwa.
Ya kuma yi alkawarin kafa fitilun masu amfani da hasken rana a kasuwar domin inganta tsaro, sannan ya bayyana wasu matakai na tallafa wa ‘yan kasuwa a jihar Jigawa, wadanda suka hada da samar da reshen bankin masana’antu (BOI) a jihar da kuma sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da bankin, inda gwamnatin jihar ta zuba naira biliyan 4 domin tallafa wa masu kananan sana’o’i.
Namadi ya kuma bukaci ’yan kasuwa a jihar da su yi amfani da wannan wurin su samu kudaden da kungiyar ta BOI ke da su don fadada kasuwancinsu.
A nasa jawabin shugaban kungiyar ‘yan kasuwa ta jihar Jigawa Alhaji Yahaya Ibrahim ya yabawa gwamnan bisa samar wa kasuwar wutar lantarki da hasken rana da kuma shirye-shiryen karfafawa ‘yan kasuwa daban-daban.
Ya kara da cewa aikin samar da wutar lantarkin kasuwar ya kasance farkon shirin Gwamna Namadi ga ‘yan kasuwa a jihar.
Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, wani bangare na aikin, na sanya na’urar samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana, mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ne ya kaddamar da shi a shekarar da ta gabata yayin wata ziyarar aiki da ya kai jihar, kuma a lokacin gwamnatin jihar ta yi alkawarin sa wutar a rumfuna kowa da kowa.
USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: lantarkin hasken rana amfani da hasken rana yan kasuwa a jihar da wutar lantarki a jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
An sake tabbatar wa ma’aikatan Gwamnatin Tarayya FG da suka yi ritaya cewa za a biya su wani bangare na kudaden ariyas a cikin wannan watan, kamar yadda hukumomin da abin ya shafa suka yi alkawari.
Mataimakin Sakataren ƙungiyar masu karɓar fansho ta ƙasa, Alhaji Ahmed Gazali, ya bayar da wannan tabbaci yayin da ake tattaunawa da shi ta wayar tarho daga Abuja.
Alh. Ahmed Gazali, ya yi bayanin cewas daraktan dake kula da kudade na ofishin akanta janar na tarayya ya tabbatar da daukan matakin hakan na biyan kudaden.
Ya bayyana fatan ganin kudirin FG na gaggauta biyan kudade, domin dakatar da duk wata zanga zanga wanda hakan bai dace ba ga ma’aikatan da suka yi ritaya domin bata martaban kasan nan.
Hakan kuma masu karban fensho a Radion Tarayya na kasa FRCN da Gidan talabijin na kasa NTA dake Kaduna sun nuna damuwarsu game da zargin da ake yi cewa ana kokarin wulakanta shugabannin kungiyar ma’aikatan da suka yi ritaya karkashin jagorancin kwamaret Munkaila Ogunbote.
DAGA SULEIMAN KAURA