Dole ɗalibi ya kawo ‘Project’ ɗinsa kafin zuwa NYSC —Gwamnati
Published: 29th, September 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya wajabta wa ɗaliban da suka kammala karatu mika kundin bincikensu na ƙarshe a matsayin sharaɗi kafin a tura su aikin yi wa kasa hidima (NYSC).
Dokar za ta fara aiki ne daga ranar 6 ga Oktoba, 2025, kamar yadda Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume ya sanar.
Ya bayyana cewa dokar ta shafi duk ɗaliban ajin ƙarshe da suka cancanci zuwa NYSC ko da kuwa a ƙasashen waje suka kammala karatu.
Wannan yana daga cikin sauye-sauyen da Gwamnatin Tarayya ta yi wanda ya alaƙanta aikin Yi wa Ƙasa Hidima (NYSC) da Tsarin Tattara Bayan Ilimi ma Kasa (NERD).
Ranar Laraba jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai dawo aiki Shekara 1 bayan rushewa, har yanzu ba gyara titin Kano–Maiduguri baBisa haka, daga yanzu babu ɗalibin da za sahalewa zuwa NYSC ba tare da ya miƙa takardar shaidar kammala binciken karshe na kammala digirinsa ba.
Gwamnatin Tarayya ta ce hakan zai taimaka wajen yakar matsalar amfani da takardun kammala karatu na bogi da kuma adana ilimi da bincike a ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Gwamnatin Tarayya
এছাড়াও পড়ুন:
Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu
Jakadan kasar Aljeriya a MDD ya gabatar da jawabi a kwamitin tsaro na majalisar a jiya Talata, inda ya yi tir da hare-haren da HKI take ci gaba da kaiwa kan Gaza, da Lebanon duk tare da yarjeniyar da ta cimma na tsagaita wuta da kungiyoyin Hizbullah da Hamas.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Ammar Ben Jamaa jakadan kasar Aljeriya a MDD yana cewa HKI ba ta mutunta yarjeniyoyin da ta cimma da kasashen Larabawa a yankin, sannan masu shiga tsakanita da wadannan kungiyoyin sun kasa tabuka wani abu na ganin bangarorin biyu sun mutanen hakkin ko wani banagare.
Jamaa ya kara da cewa a halin yanzu HKI tana kai hare-hare a kan kasashen larabawa da dama a lokaci guda, daga cikin har kan kungiyar Hizbulla, da falasdinawa a kudancin kasar Lebanon, Falasdinaw, kan Falasdinawa a Gaza da Falasdinawa a yamma da kogin Jordan da kuma kasar Siriya.
A jawabin taron karshen ko wani wata, wanda kwamitin tsaron yake yi, dangane da abubuwan da ke faruwa a yankin Asiya ta kudu, Ammar Jamaa ya ce HKI har yanzun tana kissan kare dangi na zirin gaza, sannan falasdinawa a yankin suna dab da sake shiga karancin abinci ko yunwa da kuma mummunan yanayi saboda rufe kofofin shigar kayakin bukatun Falasdinawa a yankin wanda HKI ta ke ci gaba da yi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru Mafaka Ta Wucin Gadi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin November 25, 2025 An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci