Ana zargin ’yan sanda da kashe limami a Kano
Published: 29th, September 2025 GMT
Al’ummar unguwar Kuntau da ke Ƙaramar Hukumar Gwale a Jihar Kano, sun shiga jimami bayan rasuwar wani matashin limami, Salim Usman, wanda ake zargin ya rasu a hannun ’yan sanda.
An kama Salim mai shekara 24 a gidansa a ranar 22 ga watan Satumba, jim kaɗan bayan jagorantar sallar Magariba.
2027: APC za ta ƙwace Kano ba tare da taimakon Kwankwaso ba – Jigon APC Sojoji sun kama mai yi wa Boko Haram safarar man fetur a BornoAn zarge shi da siyan buhun fulawa, wadda aka ce an sace a bara.
Mahaifinsa, Sheikh Adam Usman, ya bayyana cewa bidiyon na’urar CCTV ya nuna yadda jami’an ’yan sanda biyu suka yi wa ɗansa dukan tsiya a lokacin da suka zo su kama shi.
Ya ƙara da cewa an ci gaba da dukansa a ofishin ’yan sanda, wanda hakan ya yi sanadin mutuwarsa.
Sheikh Usman, ya ce wani abokin Salim ya bi jami’an zuwa ofishin ’yan sanda, sannan daga baya ya sanar da shi abin da ke faruwa.
Ya ce ya garzaya ofishin a daren da aka kama shi, amma aka hana shi ganin ɗansa, aka ce ya dawo washegari.
“Da na koma washegari, suka ce min ɗana ya yi rashin lafiya a daren da ya gabata aka kai shi asibiti. Amma daga baya na gano cewa tuni ya rasu.
“Da farko, an kai gawarsa Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhammad a matsayin gawar ‘wanda ba a sani ba,’ amma aka ƙi karɓa.
“Sai aka kai shi Asibitin Ƙwararru na Abdullahi Wase, inda aka ajiye shi a ɗakin ajiye gawarwaki,” in ji mahaifin matashin limamin.
Ya cw tuni suka kai ƙara hukumar ’yan sanda, kuma an shaida musu cewa an kama wasu jami’ai bisa rashin ƙwarewa a aikinsu, ana kuma gudanar da bincike.
An bayar da gawar Salim a ranar 26 ga watan Satumba, domin a binne shi bayan kotu ta bayar da umarnin a yi gwaji a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano.
Sakamakon gwajin zai fito cikin makonni huɗu.
Mutanen unguwar sun bayyana marigayin a matsayin mutum mai sauƙin kai da son zaman lafiya, inda suka ce mutuwarsa ta jefa su cikin damuwa.
Ƙoƙarin samun jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ci tura zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Gawa zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
Sojoji sun kashe ’yan ta’addan Boko Haram 9 tare da kwato kudi fansa kimanin Naira miliyan 5 a yankunan Magumeri da Gajiram a jihar Borno.
Kakakin rundunar Operation Hadin Kai (OPHK), Laftanar Kanar Sani Uba , ya ce sojojin da suke sintiri a yankunan ne suka hallakan mayakan bayan sahihan bayanan sirri kan zirga-zirgar ’yan ta’addan a kusa da Goni Dunari a Karamar Hukumar Magumeri.
Sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, 11 ga Oktoba, 2025 ta ce, “Dakarun mu sun yi gaggawar daukar matakin dakile barazanar bayan da suka ga yadda ’yan ta’addan suka kona gidaje tare da tsoratar da mutanen yankin.”
Ya bayyana cewa sojoji sun yi artabu da ’yan ta’addan ne bayan sun shafe sa’o’i hudu suna bibiyar su, inda suka kashe mayaka biyar tare da tilasta wa sauran tserewa.
Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar Neja Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoniKayayyakin da aka kwato sun haxa da bindiga kirar AK-47, alburusai, wuqa, da wayar hannu.
Uba ya qara da cewa “Babu asarar rayuka ko asarar kayan aiki da sojojin mu suka yi.”
A wani samamen kuma a hanyar Gajiram Bolori – Mile 40 – Gajiganna, sojoji sun yi arangama da mayakan Boko Haram a kusa da kauyen Zundur, inda suka kashe ’yan ta’adda hudu tare da kubutar da wasu mutane biyu da aka yi garkuwa da su daga Guzamala.
Kayayyakin da aka kwato sun hada da wata mota, sabbin wayoyin hannu guda biyu, man fetur lita 30, da tsabar kudi da suka kai Naira miliyan 4.35.
Binciken farko ya nuna cewa ’yan ta’addan sun bukaci naira miliyan 2 da wayoyi biyu a matsayin kudin fansa ga dan uwan wadanda suka kama kafin sojojin su kai dauki.
Laftanar Kanar Uba ya tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyuka matsin lamba kan ’yan ta’addan tare da hana su sakat.