Aminiya:
2025-10-13@17:53:42 GMT

Ɗalibi ya kashe malaminsa har lahira a Kuros Riba

Published: 27th, September 2025 GMT

Wani ɗalibi mai suna Ogbeche, ya kashe malaminsa Oshen, a makarantar sakandire da ke garin Ugboro, da ke Ƙaramar Hukumar Bekwarra a Jihar Kuros Riba.

Rahotanni sun nuna cewa malamin ya yi ƙoƙarin raba faɗa tsakanin Ogbeche da wani ɗalibi.

Ma’aikatan jinya sun tsunduma yajin aiki a Zamfara Matatar Ɗangote ta dakatar da sayar da fetur a farashin Naira

Sai dai a fusace, ɗalibin ya fisge taɓarya daga hannun wata mata, ya buga wa malamin a kai, wanda hakan ya sa ya faɗi sumamme.

Duk da garzayawa da shi da aka yi zuwa asibiti, likitoci sun tabbatar da mutuwarsa.

Wata ganau mai suna Lizzy ta ce: “Malamin kawai yaje rabon faɗa ne, amma Ogbeche ya fusata ya ɗauki taɓarya ya buga masa a kai, nan take ya faɗi.”

Al’ummar yankin sun nuna ɓacin ransu, inda suka ce abin da ɗalibin ya aikata ba abin yadda ba ne, domin ya hallaka malaminsa.

Yanzu haka, rundunar ’yan sandan jihar, ta kama Ogbeche, inda ake masa tambayoyi kafin a miƙa shi zuwa hedikwatar rundunar domin ci gaba da bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibi Faɗa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

Sojojin Nijeriya sun kashe wani kwamandan ƙungiyar ƴan ta’adda IPOB/ESN da ake nema ruwa a jallo, mai suna ‘Alhaji’, tare da wasu mutane 26 a jerin hare-haren da suka kai a sassan ƙasar tsakanin 8 zuwa 11 ga Oktoba, 2025. Rundunar Sojin ta ce an kuma ceto mutane biyar da aka yi garkuwa da su, tare da kwace makamai, da harsasai, da kuɗaɗe.

A kudu maso gabas, Sojojin Operation UDO KA sun kai farmaki a Izzi, jihar Ebonyi, inda suka kashe ‘Alhaji’ bayan ya yi yunƙurin kwace bindiga daga hannun wani Soja lokacin kama shi. Haka kuma, a jihar Imo, an rusa wata maboyar IPOB/ESN da ake amfani da shi wajen horar da mambobi.

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

A Arewa maso gabas, Sojojin Operation Haɗin Kai sun kashe ‘yan ta’adda tara a Magumeri da Gajiram a jihar Borno, inda suka ceto fararen hula biyu tare da ƙwato fiye da Naira ₦4.3 miliyan. A wasu hare-haren sama a jihar Sokoto, an hallaka shugabannin ‘yan ta’adda da dama, yayin da aka kama masu safarar miyagun ƙwayoyi daga Legas zuwa Zamfara.

A Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Kudu, Sojojin Operation Whirl Stroke da Operation DELTA SAFE sun kama masu garkuwa da mutane, sun kashe ‘yan ƙungiyar asiri biyu, kuma sun ƙwato makamai da babura. Rundunar Sojin ta ce gaba ɗaya an kashe ‘yan ta’adda 26, an kama mutum 22, kuma an ceto mutane biyar da aka yi garkuwa da su.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato October 11, 2025 Tsaro Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno October 11, 2025 Tsaro Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga Dan Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya.
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta
  • Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole