Aminiya:
2025-11-27@21:46:51 GMT

HOTUNA: An kai gawar Arase Benin domin yi mata jana’iza

Published: 27th, September 2025 GMT

An kai gawar Tsohon Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Solomon Arase, zuwa Birnin Benin, Babban Birnin Jihar Edo, domin yi masa  jana’iza.

Arase, ya rasu ne a ranar 31 ga watan Agusta, 2025, a Asibitin Cedarcrest da ke Abuja, bayan fama da rashin lafiya.

Mutum 7 sun rasu yayin da tirela ta murƙushe motoci a Madalla ’Yan uwa sun samu Digiri Mai Daraja ta Ɗaya a fanni iri ɗaya 

A makon da ya gabata, aka gudanar da bikin tunawa da shi a Abuja.

Sai kuma a ranar Asabar Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta kai gawarsa Benin domin kammala bukukuwan jana’izarsa.

Ga hotuna:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arase rasuwa Tsohon Sufeto Janar Na Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina

Hukumar kula da makarantun firamare da sakandare ta Jihar Katsina ta sanar da sake buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarabawar zangon farko na shekarar karatu.

A wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Sani Danjuma Suleman, ya fitar a madadin Shugaban hukumar, ta ce makarantun firamare, sakandiren je-ka-ka-dawo da kuma makarantu masu zaman kansu za su buɗe daga yau Talata domin ci gaba da jarabawar zangon farko.

Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran makarantun kwana za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai lokacin da hali ya ba da dama.

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Gwamnatin Katsina ta rufe makarantun bayan ƙaruwar hare-haren sace ɗalibai da masu garkuwa da mutane suka sake farfaɗowa da su a wasu yankuna.

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne da nufin daƙile matsalar tsaro da kuma sa ido a kan al’amura.

A ƙarshe, hukumar ta roƙi haɗin kan iyaye da masu kula da ɗalibai domin su ci gaba da ba wa shirin goyon baya tare da ƙarfafa ɗaliban su dage da karatu wajen rubuta jarabawar da suke yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra
  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin