’Yan uwa sun samu Digiri Mai Daraja ta Ɗaya a fanni iri ɗaya
Published: 27th, September 2025 GMT
Wane irin farin ciki za ku ji a matsayinku na iyaye, a cewa ’ya’yanku biyu sun kammala jami’a da Digiri Mai Daraja ta Ɗaya (First Class) a lokaci guda kuma daga wani kwas mai farin jini a wannan zamani na kimiyyar zamani?
Wani labari mai sha’awa shi ne yadda wasu ’yan uwa biyu suka kammala karatun jami’ansu da maki iri ɗaya a matakin Digiri Mai Daraja ta Ɗaya a wannan shekarar daga jami’o’i daban-daban.
Maryam Salisu da yayanta Suleiman Salisu kowannensu ya kammala karatun digirinsa na farko ne da maki 4.51 daga fannin Kimiyyar Kwamfuta, a wannan shekara ta 2025 a Jihar Katsina.
A halin yanzu Suleiman ya fara aikin Yi wa Ƙasa Hidima (NYSC) a yayin da ƙanwar tasa take jiran lokacin tafiyarta.
Maryam ta kammala karatunta ne daga Jami’ar Tarayya da ke Dutsin-ma a Jihar Katsina a yayin da Suleiman ya halarci Jami’ar Al-istiƙama da ke jihar ta Katsina.
Game da yadda aka yi suka samu maki iri ɗaya ta yayanta, Maryam wadda suke zaune a Abuja, ta ce, “Gaskiya ba wani shiri muka yi ba, Allah ne Ya ƙaddara faruwar hakan. Kuma mun yin murna da wannan nasara, mun faranta wa iyaye da ’yan uwanmu rai,” in ji ta.
Abin da ya ƙara min ƙwarin gwiwaA hirarsu da Aminiya, Maryam, ta ce wasu sun yi mamakin yadda ta zaɓi ta karanci fannin Kimiyyar Kwamfuta alhali kwas ne da ake ganin maza ne ke tururuwar karanta shi.
Ta bayyana cewa ita da kanta ta zaɓi ta karanci kwas domin tana da sha’awar zama ɗaya daga cikin waɗanda za a dama da su a ɓangaren kimiyya da fasaha kuma tana da burin karantar abin da ya shafi ƙiƙirarriyar basira (AI).
Ta ce a lokacin da wasu suka ji kwas ɗin ta take son karantawa sun yi ƙoƙarin karya ƙwarin gwuiwarta, cewa kwas ne da mata ba su fiye yi ba saboda wahalarsa, amma sai hakan ya ƙara mata ƙarfin gwuiwar cika burinta, saboda tana so ta nuna cewa babu wani fannin ilimi da ya fi ƙarfin mace ta karanta.
Da aka tambaye ta ko ta yarda da cewa Suleiman ya fita ta hazaƙa, sai ta ce: “Eh, duk da cewa ina mishi dariya idan na ga yana hana kansa barci a lokacin, amma gaskiya yana aiki tuƙuru kuma yana da hazaƙa.
“Idan ban fahimci abu ba, sai ya koya mun da kansa. Wannan shi ne abin da nake matuƙar yaba masa a kai.”
‘Ba na iya barci’Da yake bayyana wa wakilinmu irin faɗi tashin da ya yi a lokacin da yake makaranta, Suleimin ya bayyana yadda yake karatu wurjanjan tare da hana idonsa barci.
“Ni dai na sha wahala, ban fiye yin barci ba. Ba na kwanciya barci. Abin da ya kai ni ga wannan nasarar shi ne jajircewa da yin aiki tuƙuru da kuma dogaro ga Allah.”
Suleiman da Maryam sun bayyana cewa duk da cewa daban-daban kowannensu yake karatunsa, amma suna yawan tattaunawa da taimakon juna wajen karatu, musamman tun da tsarin karatunsu na kama da juna.
Game ya yaba da ƙwazon ƙanwar tasa, ya ce, “Eh, kowa ya san fannin nan maza ne suka fi yawa. A ajinmu, muna da mace ɗaya kacal daga cikin sama da mutum 50. Amma hakan ba ya nufin mace ba za ta iya ba. A gaskiya muna da buƙatar mata a wannan fanni, kuma ina alfahari da ƙanwata.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Digiri Mai Daraja ta Ɗaya
এছাড়াও পড়ুন:
Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
Hukumar tsaro ta DSS ta zargi dan jarida kuma mai shiga tsakani da ’yan ta’addar da suka sace fasinjojin jrigin kasan Kaduna-Abuja a shekarar 2022, Tukur Mamu, da karbar Naira miliyan 50 daga kudin fansar fasinjojin.
Ana zargin Tukur Mamu da karbar kudin ne daga jagoran ’yan bindigar da ake kira da “Shugaba”.
Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000 Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan KebbiMamu na fuskantar tuhumar laifukan ta’addanci, ciki har da karɓar kuɗin fansa daga iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su a harin jirgin Kaduna na ranar 28 ga Maris, 2022, hulɗa da kuɗaɗen ’yan ta’adda, hana aikin kwamitin babban hafsan tsaron kasa da aka kafa domin tattaunawa da masu garkuwa da mutanen, musayar saƙonnin murya da mai magana da yawun Boko Haram, da sauransu.
A ci gaba da shari’ar a ranar Talata, shaida na hukumae ta DSS na shida ya shaida wa kotu cewa ƙungiyar ta’addan ta nemi Mamu ya koya musu yadda ake buɗe shafin yanar gizo domin gudanar da ayyukansu.
Tun da farko, DSS ta bayyana cewa Mamu ya ba da shawara ga ƙungiyar ’yan ta’addan da su tattauna kai tsaye da iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su, ba tare da shiga kwamitin babban hafsan tsaron da gwamnatin tarayya ta kafa ba.
Shaidar ya yi wannan bayani ne yayin fassara saƙonnin murya na Mamu a lokacin da ake yi masa tambayoyi a ƙasar Masar kafin a dawo da shi Najeriya.
A halin yanzu, Mamu ya shigar da Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN) kara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, bisa kiran shi da dan ta’adda.
Ya ce ya shigar da ƙarar ce kan kiran nasa da dan ta’adda da ministan ya yi, alhali ana tsaka da shari’ar tuhumar laifukan ta’addanci kuma har yanzu ba a kai ga yanke hukunci ba.
Alƙali ya dage shari’ar zuwa ranar 23 ga watan Fabrairun 2026, domin amincewa da jawaban ƙarshe na ɓangarorin da abin ya shafa bisa tanadin Sashe na 49 na Dokar da kuma Sashe na 36 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.