Ƙasashen duniya sun ƙaurace wa Isra’ila a Babban Taron MƊD
Published: 27th, September 2025 GMT
Wakilan ƙasaahen duniya sun ƙaurace wa jawabin Shugaban Ƙasar Isra’ila Benjamin Netanyahu, a taron Majalisar Ɗinkin Duniya domin su nuna goyon bayansu ga al’ummar Palasɗinawa.
Fiye da rabin wakilan da suka halarci Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA) sun miƙe tare da ficewa daga zauren taron ne a yayin da Mista Netanyahu yake shirin gabatar da jawabin ƙasarsa ta Isra’ila.
Zauren taron ya kasance kusan wayan, in banda ’yan jarida da jami’an MƊD da wasu tsirarun wakilan ƙasashe da suka rage a ciki a lokacin jawabin Mista Netanyahu wanda Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC) ta ba da umarnin kamo shi domin gurfanarwa kan laifukan yaƙi a Zirin Gaza inda dakarun Isra’ila suka kashe mutane kimanin 79,000, akasarinsu ƙananan yara da tsofaffi da kuma mata— baya ga jikkata wasu fiye da hakan.
Ƙauracewar ƙasashen domin nuna fushi ga Isra’ila ta faru ne a bayan ƙarin manyan ƙasashen duniya kuma ƙawayen Isra’ilar, irin su Faransa da Ingila da Kanada sun sanar da taron na MƊD game goyon bayansu ga batun kafa ƙasar Palasɗinu mai cikakkiyar ’yanci.
Hakan ta faru ne kwanaki kaɗan bayan rohoton kwamitin bincike da Majalisar Ɗinkin Duniya ta kafa kan mamaya da yaƙin da Isra’ila ta shafe shekara biyu tana yi a Gaza ya samu shugabanni da sojojin Isra’ila da laifin yi wa Falasɗinawa kisan ƙare dangi.
Baya ga kisan mutane kimanin 70,000 — wasunsu a asibitoci da makarantu da sansanonin ’yan gudun hijira da wuraren da Isra’ila ta ayyana a matsayin masu aminci a Gaza, jirage da tankokin yaƙin Isra’ila sun rushe gidajen sama da mutum miliyan ɗaya, baya ga wuraren ibada da makarantu da asibitoci da sauran wuraren taruwa jama’a.
Kazalika Isra’ila ta lalata abubuwan more rayuwa, kamar ruwan sha da wutar lantarki da sufuri, haka kuma ta hana shigo da kayan agaji — na abinci da magunguna da sauransu — zuwa Gaza.
Netanyahu ya bayyana cewa ƙasarsa ba za ta dakatar da yaƙin ba har sai ta ƙwace Gaza ta murƙushe ƙungiyar Hamas sa’annan ta ƙwato ’yan ƙasarta da ƙungiyar ta yi garkuwa da su tun ranar 7 ga Oktoba, 2023, inda Hamas ta kai mata harin ba zata, ta kashe mutane 1,200 tare da sace wasu kimanin 250.
Ƙasashe da dama sun la’anci ayyukan Isra’ila a Gaza, a rikicin da ya samo asali sama da shekaru 40 da suka wuce, kan mamaye ƙasar Palasɗinu da Isra’ila take yi, tana kafa wa Yahudawa matsugunan kama-wuri-zauna.
Tun lokaci mai tsawo, kasashe da hukumomin duniya sune ta nananta cewa kafa ƙasashe biyu — Palasɗinu mai ’yanci da kuma Isra’ila, a matsayin mafita ga rikicin wanda ya ƙi ci ya ƙi cinyewa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Isra ila kisan ƙare dangi Ƙasashe ƙaurace wa Isra ila Palasɗinawa taron Majalisar Ɗinkin Duniya Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Dr Ali Larijan wanda ya ke ziyarar aiki na kwanaki uku a kasar Pakistan ya yabawa kasar saboda goyon bayan da ta bawa kasarsa a lokacin yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka dorawa kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Dr Ali Larijana yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Talata. Sannan yace ya isar da sakon gaisuwa na Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khami’ae ga mutanen kasar Pakistan. Banda haka ya gana da Firai ministan kasar Shehbaz Sharif da shugaban kasa Asif Ali Zardari da kuma kakakin majalisar dokokin kasar kasar Sardar Avaz Saadik.
A ganawar Larijani da Sharif sun tattauna kan dangantaka mai tsawo da ke tsakanin Iran da Pakisatan, da kuma bukatar a kara zurfafata.
Sharif a nasa bangaren ya bayyana cewa nan ba da dadewa waministan harkokin wajen kasar Mohammad Ishak Dar zai ziyarci Tehran inda ake saran zai rattaba hannu kan yarjeniyoyi na bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu, daga ciki har da batun kammala aikin shimfida bututun gas daga kasar Iran zuwa Pakistan. Da kuma harkokin sadarwa.
A cikin wannan shekarar ne dai kasashen biyu suka rattaba hannu kan yarjeniyar bunkasa kasuwanci ta dalar Amurka billion 10 a tsakaninsu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru Mafaka Ta Wucin Gadi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin November 25, 2025 An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci