Ƙasashen duniya sun ƙaurace wa Isra’ila a Babban Taron MƊD
Published: 27th, September 2025 GMT
Wakilan ƙasaahen duniya sun ƙaurace wa jawabin Shugaban Ƙasar Isra’ila Benjamin Netanyahu, a taron Majalisar Ɗinkin Duniya domin su nuna goyon bayansu ga al’ummar Palasɗinawa.
Fiye da rabin wakilan da suka halarci Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA) sun miƙe tare da ficewa daga zauren taron ne a yayin da Mista Netanyahu yake shirin gabatar da jawabin ƙasarsa ta Isra’ila.
Zauren taron ya kasance kusan wayan, in banda ’yan jarida da jami’an MƊD da wasu tsirarun wakilan ƙasashe da suka rage a ciki a lokacin jawabin Mista Netanyahu wanda Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC) ta ba da umarnin kamo shi domin gurfanarwa kan laifukan yaƙi a Zirin Gaza inda dakarun Isra’ila suka kashe mutane kimanin 79,000, akasarinsu ƙananan yara da tsofaffi da kuma mata— baya ga jikkata wasu fiye da hakan.
Ƙauracewar ƙasashen domin nuna fushi ga Isra’ila ta faru ne a bayan ƙarin manyan ƙasashen duniya kuma ƙawayen Isra’ilar, irin su Faransa da Ingila da Kanada sun sanar da taron na MƊD game goyon bayansu ga batun kafa ƙasar Palasɗinu mai cikakkiyar ’yanci.
Hakan ta faru ne kwanaki kaɗan bayan rohoton kwamitin bincike da Majalisar Ɗinkin Duniya ta kafa kan mamaya da yaƙin da Isra’ila ta shafe shekara biyu tana yi a Gaza ya samu shugabanni da sojojin Isra’ila da laifin yi wa Falasɗinawa kisan ƙare dangi.
Baya ga kisan mutane kimanin 70,000 — wasunsu a asibitoci da makarantu da sansanonin ’yan gudun hijira da wuraren da Isra’ila ta ayyana a matsayin masu aminci a Gaza, jirage da tankokin yaƙin Isra’ila sun rushe gidajen sama da mutum miliyan ɗaya, baya ga wuraren ibada da makarantu da asibitoci da sauran wuraren taruwa jama’a.
Kazalika Isra’ila ta lalata abubuwan more rayuwa, kamar ruwan sha da wutar lantarki da sufuri, haka kuma ta hana shigo da kayan agaji — na abinci da magunguna da sauransu — zuwa Gaza.
Netanyahu ya bayyana cewa ƙasarsa ba za ta dakatar da yaƙin ba har sai ta ƙwace Gaza ta murƙushe ƙungiyar Hamas sa’annan ta ƙwato ’yan ƙasarta da ƙungiyar ta yi garkuwa da su tun ranar 7 ga Oktoba, 2023, inda Hamas ta kai mata harin ba zata, ta kashe mutane 1,200 tare da sace wasu kimanin 250.
Ƙasashe da dama sun la’anci ayyukan Isra’ila a Gaza, a rikicin da ya samo asali sama da shekaru 40 da suka wuce, kan mamaye ƙasar Palasɗinu da Isra’ila take yi, tana kafa wa Yahudawa matsugunan kama-wuri-zauna.
Tun lokaci mai tsawo, kasashe da hukumomin duniya sune ta nananta cewa kafa ƙasashe biyu — Palasɗinu mai ’yanci da kuma Isra’ila, a matsayin mafita ga rikicin wanda ya ƙi ci ya ƙi cinyewa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Isra ila kisan ƙare dangi Ƙasashe ƙaurace wa Isra ila Palasɗinawa taron Majalisar Ɗinkin Duniya Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya tafi birnin Rome na Ƙasar Italiya, domin halartar taron shugabannin ƙasashe kan sha’anin tsaro.
Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin labarai, Bayo Onanuga, ya ce za a fara taron ne a ranar 14 ga watan Oktoba, kuma zai mayar da hankali kan matsalar tsaro da ke addabar yankin Yammacin Afirka.
’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — KwamishinaTaron na ‘Aqaba Process’ an kafa shi ne a shekarar 2015 ta hannun Sarki Abdullah II na Ƙasar Jordan, kuma ana gudanar da shi tare da haɗin gwiwar Jordan da ƙasar Italiya.
Taron na nufin tattauna hanyoyin yaƙi da ta’addanci da kuma magance matsalolin tsaro da ke adabbar ƙasashe daban-daban, musamman a yankin Yammacin Afirka.
Taron zai haɗa shugabannin ƙasashe na Afirka, jami’an leƙen asiri da na tsaro, da wakilan ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na ƙungiyoyin fararen hula, domin tattauna yadda za a magance matsalolin tsaro da ke addabar yankin.
Za a tattauna kan yadda ƙungiyoyin ta’addanci ke yaɗuwa a Yammacin Afirka, alaƙa tsakanin masu laifi da ’yan ta’adda, da kuma alaƙar da ke tsakanin ta’addanci a yankin Sahel.
Hakazalika, za a tattauna yadda za a daƙile yaɗuwar aƙidar ta’addanci a Intanet da kuma lalata hanyoyin sadarwar da ’yan ta’adda ke amfani da su wajen yaɗa ra’ayoyinsu da ɗaukar sababbin mabiya.
Shugaba Tinubu zai kuma tattauna da wasu shugabannin ƙasashe don neman hanyoyin daƙile matsalar tsaro da ke addabar yankin.
Tinubu ya samu rakiyar Ministan Harkokin Waje, Ambasada Bianca Odumegwu–Ojukwu; Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar.
Sauran sun haɗa daMai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu; Darakta-Janar na Hukumar Leƙen Asiri ta Ƙasa (NIA), Ambasada Mohammed Mohammed; da wasu manyan jami’an gwamnati.