Bisa sashe na 154 (1) na kundin tsarin mulkin na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, ” shugaban kasa ne zai nada shugaban INEC da mambobin hukumar zabe ta kasa, sannan majalisar dattawa ta tabbatar da su.”

Dangane da tanadin da ke cikin tsarin mulki, Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa ya tanadi jerin sunayen ‘yan takara da za su meye gurbin Yakubu.

Da yake jawabi kan tsammanin jam’iyyar APC mai mulki, daraktan yada labarai, Bala Ibrahim, ya bayyana cewa yayin da jam’iyyar ke nufin lashe duk zabe, tana jaddada bukatar samun yin aldaci ga kowa.

Ibrahim, a cikin wata hira, ya bayyana cewa, “A matsayinmu na jam’iyya, abin da muka sa a gaba shi ne samun nasarar cin zabe mai cike da inganci.”

“Babban burinmu shi ne, yadda za mu karbe iko ta hanyar da za ta ba da riba ga dimokuradiyya ga mutane. burinmu ita ce yadda za mu tsaya takara a zabe kuma a ba mu damar taka ba tare da an dakatar da mu ko an cire mu daga zabe ba.

“Don haka, muna sa ran samun shugaban hukumar zabe wanda zai ba da dama ga kowa, wanda zai ba da damar gudanar da zabe cikin ‘yanci da adalci. Muna bukatar shugaban INEC da zai yi aiki ka doka.”

Sakataren yada labarai jam’iyyar PDP, Debo Ologunagba, ya jaddada cewa dole ne shugaban INEC da zai zo ya zama mutum mai nagarta.

Ologunagba ya kuma kira ga shugaban kasa da masu ruwa da tsaki masu alkakkin zaben shugaban INEC su yi la’akari da halayen ‘yan takarar sosai kuma su tabbatar an nada mutumin da ke da kwarewa.

Ya bayyana cewa, “Shugaban INEC na gaba ya zama wani mutum mai nagarta, ya zama wanda ba zai kasance mai mummunan hali ba, ya zama mai adalci, wanda zai zama mai ‘yanci kuma ya gudanar da hukumar ta wannan hanyar, kamar yadda doka ta tanada. Don haka wannan shi ne abin da muke tsammani.”

Ita kuwa jam’iyyar hadaka, ta bakin sakataren yada labarai na kasa, Bolaji Abdulahi, ta bayyana damuwa kan rikicin bai wa INEC ‘yancin kanta.

Abdullahi ya bayyana cewa sabon shugaban INEC da za a zaba dole ne ya yi aiki don dawo da amincewa ta hanyar tabbatar da gudanar da zabe mai inganci a 2027.

Ya ce, “Abu mafi muhimmanci shi ne, ina tunanin INEC ta sha fama da rikice-rikice na samun amincewa a idon masu kada kuri’a a Nijeriya a cikin shekaru da dama.”

“Sabon shugaban INEC ya kamata ya tabbatar da cewa hukumar ta ci gaba da kasancewa a matakin amincewa. Ka san cewa, tabbatar da tsarin zabe yana karfafa gwiwar kowa, kuma shi ne kawai hanyar da za a tabbatar da kwanciyar hankali a cikin kasar nan.

“Dole ne su tabbatar da nada mtumin da zai kasance tsayayye da kuma jajircewa. Idan aka kasa yin hakan, hakan na iya haifar da shakku a cikin zukatan ‘yan kasa game da ingancin zaben 2027, ko za su kasance masu ‘yanci da adalci kan zaben.

“Don haka, ina tsammanin shekara ta 2027 za ta zama mai muhimmanci ga kowa. A matsayin jam’iyya, muna fatan cewa nadin zai ba da damar ga wanda ya fahimci muhimmancin tarihi na aikin.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Siyasa ya bayyana cewa tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina

Ana zargin wata amarya da yi wa angonta yankan rago kwana uku bayan ɗaurin aurensu a Jihar Katsina.

Angon mai suna Abubakar Abdulkarim da aka fi sani da Dan Gaske, ana zargin ya rasa ransa bayan da amaryar ta yi amfani da wuƙa wajen halaka shi.

Shaidu sun ce ta yi masa mummunan rauni a wuya wanda ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Angon da amaryarsa suka daura aure ne a ranar Alhamis, 18 ga Nuwamba, 2025, amma farin cikin aure ya rikide zuwa makoki a ranar Lahadi da rana lokacin da lamarin ya faru.

Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta

Wani ɗan uwansa mai suna Aminu Danladi ya ce cewa sun yi taro da marigayin da safiyar ranar, suna shirya ziyarar ’yan uwansu da za a kai da yamma.

Ya ce daga baya ango ya koma gida domin shiri, sai kuma aka ji labarin an same shi kwance a cikin jini babu rai.

Aminu ya kuma ƙaryata jita-jitar da ake yaɗawa cewa auren dole ne aka yi wa ma’auratan, inda ya tabbatar da cewa dangantakarsu ta kasance lafiya kafin aure.

Majiyoyi sun ce matar, ’yar asalin Katsina, ta taɓa yin aure a baya, abin da ake zargin dangin mijin ba su sani ba.

An ce bayan faruwar lamarin amaryar ta ruɗe inda ta je gidan maƙwabta tana neman abinci. Wannan hali ya sa tsofaffin mata zargin akwai matsala, suka bi ta gida inda suka tarar da gawar mijin, suka kuma sanar da jami’an tsaro.

Rundunar ’Yan Sanda ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce ta fara gudanar da bincike a kai.

Kakakin ’yan sanda na jihar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce an kama mutum ɗaya da ake zargi da hannu a lamarin, kuma bincike na ci gaba.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Katsina, CP Bello Shehu, ya tabbatar da cewa za a gudanar da bincike mai zurfi, tare da kira ga jama’a da su bayar da bayanai masu amfani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu.
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina