Aminiya:
2025-10-13@15:43:47 GMT

’Yan Najeriya da tauraronsu ya haska a Ballon d’Or

Published: 26th, September 2025 GMT

A ranar Litinin aka gudanar da bikin bayar da kyautar Ballon d’Or a Birnin Paris, inda ake karrama fitattun ’yan ƙwallon duniya.

A bana, Ousmane Dembele na Ƙasar Faransa da PSG ne, ya lashe kyautar maza, yayin da Aitana Bonmati ta Spaniya ta lashe ta mata karo na uku a jere.

An gano yarinya da aka sayar ₦3.

7m a Ondo Naɗin Olubadan: Tinubu da manyan jami’ai sun ziyarci Ibadan

Abin farin ciki ga Najeriya shi ne, mai tsaron ragar Super Falcons, Chiamaka Nnadozie, ta zo ta huɗu a jerin mata, wanda shi ne matsayi mafi girma da wata ’yar Najeriya ta taɓa samu.

Ga jerin ’yan Najeriya da suka taɓa shiga cikin jerin waɗanda suka fafata neman kyautar Ballon d’Or:

Finidi George — 1995

Ya taka leda a Ajax inda ya taimaka wajen lashe gasar Champions League. Ya zo na 21 a duniya.

Nwankwo Kanu — 1996 da 1999

Ya taimaka wa Najeriya ta lashe Olympics a Atlanta 1996, sannan ya taka rawa a Inter Milan da Arsenal. Ya zo na 11 a 1996 da na 23 a 1999.

Victor Ikpeba — 1997

“Prince of Monaco” ya taimaka wa Monaco wajen lashe gasar Ligue 1. Ya zo na 32.

Asisat Oshoala — 2022 da 2023

Ita ce mace ta farko daga Najeriya da ta shiga jerin neman kyautar Ballon d’Or. Ta zo na 16 a 2022, sannan ta zo na 20 a 2023.

Victor Osimhen — 2023

Ya jagoranci Napoli wajen lashe gasar Serie A bayan shekara 33. Ya zo na 8, sannan ya lashe gwarzon ɗan ƙwallon Afirka.

Ademola Lookman — 2024

Tauraronsa ya haska Atalanta, inda ya taimaka mata wajen lashe gasar Europa League, ya kuma zura ƙwallaye a Gasar Afirka. Ya zo na 14.

Chiamaka Nnadozie — 2025

Ta zo na 4 a cikin masu tsaron raga mata, abin alfahari ga Najeriya. Ta kuma lashe gasar Kofin Afirka sau biyu (2018 da 2024).

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Ƙwallo Najeriya wajen lashe gasar

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Na farko, hada kai don samar da yanayi mai kyau ga ci gaban mata. Na biyu, a karfafa abubuwan da za su habaka ingancin ayyukan mata cikin hadin kai. Kana na uku, a gina tsarin kare hakkin mata tare. Sai na hudu, a bude sabon babin hadin gwiwa tsakanin mata a duniya.

 

Za a gudanar da taron kolin mata na duniya a yau da gobe Talata a birnin Beijing. Kuma tuni shugaban kasar Sin Xi Jinping da uwargidansa Peng Liyuan, suka yi musafaha da shugabannin tawagogin kasashe, da kungiyoyin duniya da suka halarci taron, tare da daukar hotuna tare da su. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina October 12, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth October 12, 2025 Daga Birnin Sin An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
  • Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi
  • Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • ’Yan Najeriya miliyan 60 na fama da taɓin hankali – Likita