’Yan Najeriya da tauraronsu ya haska a Ballon d’Or
Published: 26th, September 2025 GMT
A ranar Litinin aka gudanar da bikin bayar da kyautar Ballon d’Or a Birnin Paris, inda ake karrama fitattun ’yan ƙwallon duniya.
A bana, Ousmane Dembele na Ƙasar Faransa da PSG ne, ya lashe kyautar maza, yayin da Aitana Bonmati ta Spaniya ta lashe ta mata karo na uku a jere.
An gano yarinya da aka sayar ₦3.7m a Ondo Naɗin Olubadan: Tinubu da manyan jami’ai sun ziyarci Ibadan
Abin farin ciki ga Najeriya shi ne, mai tsaron ragar Super Falcons, Chiamaka Nnadozie, ta zo ta huɗu a jerin mata, wanda shi ne matsayi mafi girma da wata ’yar Najeriya ta taɓa samu.
Ga jerin ’yan Najeriya da suka taɓa shiga cikin jerin waɗanda suka fafata neman kyautar Ballon d’Or:
Finidi George — 1995Ya taka leda a Ajax inda ya taimaka wajen lashe gasar Champions League. Ya zo na 21 a duniya.
Nwankwo Kanu — 1996 da 1999Ya taimaka wa Najeriya ta lashe Olympics a Atlanta 1996, sannan ya taka rawa a Inter Milan da Arsenal. Ya zo na 11 a 1996 da na 23 a 1999.
Victor Ikpeba — 1997“Prince of Monaco” ya taimaka wa Monaco wajen lashe gasar Ligue 1. Ya zo na 32.
Asisat Oshoala — 2022 da 2023Ita ce mace ta farko daga Najeriya da ta shiga jerin neman kyautar Ballon d’Or. Ta zo na 16 a 2022, sannan ta zo na 20 a 2023.
Victor Osimhen — 2023Ya jagoranci Napoli wajen lashe gasar Serie A bayan shekara 33. Ya zo na 8, sannan ya lashe gwarzon ɗan ƙwallon Afirka.
Ademola Lookman — 2024Tauraronsa ya haska Atalanta, inda ya taimaka mata wajen lashe gasar Europa League, ya kuma zura ƙwallaye a Gasar Afirka. Ya zo na 14.
Chiamaka Nnadozie — 2025Ta zo na 4 a cikin masu tsaron raga mata, abin alfahari ga Najeriya. Ta kuma lashe gasar Kofin Afirka sau biyu (2018 da 2024).
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Ƙwallo Najeriya wajen lashe gasar
এছাড়াও পড়ুন:
Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya
An naɗa Andrea Thompson, ’yar ƙasar Birtaniya, a matsayin mace mafi ƙarfi a duniya.
Wannan na zuwa ne bayan tabbatar da cewa wanda aka bayyana a matsayin zakara — Jammy Booker — tun da farko namiji ne da aka sauya masa halitta zuwa mace, lamarin da ya sa aka soke nasararsa bisa saɓawa dokokin gasar.
Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro Real Madrid za ta yi karon-batta da Olympiacos a Gasar Zakarun TuraiThompson mai shekaru 43, ta karɓi lambar yabon ne daga masu shirya gasar nunin ƙarfi ta duniya, kwanaki biyu bayan kammala bikin a Arlington da ke birnin Texas na Amurka, wanda aka gudanar a daga 20 zuwa 23 ga watan Nuwamba.
Gasar nuna ƙarfin ta duniya tana da tsauraran ƙa’idoji, inda ake bai wa ’yan takara damar fafatawa ne kawai bisa jinsinsu na asali domin tabbatar da adalci.
A gasar bana, Thompson ta ƙare a matsayi na biyu bayan kammala fannonin wasanni guda shida da suka haɗa da ɗaga nauyi da sauran gwaje-gwaje a rukunin mata.