Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie
Published: 25th, September 2025 GMT
Indomie, a matsayin jigo da ta daɗe wajen nasarar samar da abinci mai gina jiki ga al’umma, tana alfahari da tallafawa wannan yunƙuri na kafa tarihi na Collins. Shekaru da dama, Indomie ta tallafa wa shirye-shiryen tallafawa a fannin ƙirƙira da ilimi da sana’o’i ga matasa. Tallafawa Collins, wata alamar nasara ce da take nuna ƙoƙarin Indomie na isar da saƙo mai ƙarfi ga jama’a wajen cimma manyan burika da muradan rayuwa da suke bukatar samun goyon baya da ƙarfafa guiwa.
Shigar cikin wannan al’amari wata babbar alama ce da take tabbatar da cewa wannan taron na tarihi ya sami haske da karramawa kamar yadda ya dace, taro ne da yake ƙarfafa wa matasan Nijeriya guiwa domin su samu nasarar cimma burinsu na rayuwa ta hanyar samun ƙwarin guiwa.
An tsara taron zai gudana a Kano a Ranar samun ‘yancin mulkin ƙasa Nijeriya, inda ake sa ran jama’a da iyalai da ɗalibai da masoya fasaha da ƙirƙira da ‘yan jarida daga ko’ina a cikin ƙasa za su hallarci taron. Masu kallo za su samu damar shaida tarihin da Collins zai kafa a lokaci wajen zana fuskar mutane sama da 12 a cikin minti 3 da kuma zana fuskar mutane fiye da 220 cikin awa 1.
Wannan taro da zai samu halartar jama’a zai bunƙasa al’ada da ƙirƙira kuma zai sa ranar ta kasance ta musanman ba kawai taro kadai ba, inda ranar za ta zama muhimmiyar ranar biki ta baje-kolin nuna baiwa da samar da haɗin kai.
Ƙoƙarin kafa wannan wannan tarihin da karbe kambun zai samu goyon baya da bai wa matasa dama ta musanman. Labarin Collins zai ja hankalin matasan Nijeriya waɗanda suke da mafarkin samun shahara a duniya. Kuma zai zama wata shaida ta cimma ƙuduri bayan samun dama da ƙarfafa guiwa daga Indomie a ɓangaren fasaha a Nijeriya.
A yayin da Kano ke shirin karɓar baƙi domin gudanar da wannan gagarumin biki a wannan rana mai ɗumbin tarihi, jama’a na cike da farin ciki a harabar jami’ar da kafafen sada zumunta da wurare daban-daban. Yunƙurin Collins ba kawai nasara ce ta ƙashin kansa ba; lokaci ne na tarihi wanda ke nuna ci gaban fasahar ƙirƙira a Nijeriya a idon duniya, kuma wata ‘yar manuniya ce da take nunawa kowa cewa samun manyan nasarori na farawa ne da sha’awa da ƙuduri da kuma samun tallafi.
Taken Indomie na “Mafarki mai yawa na haifar da nasarori masu yawa” an sanya shi a cikin muradin Collins. A ranar 1 ga Oktoba, duk idanu za su koma Kano domin ganin Collins Whitworth yadda zai kafa tarihi, ba kawai ta zanen fuska ba, har ma ta bayyana irin ƙwazonsa da baiwarsa da yadda zai zama abin alfahari ga ƙasa Nijeriya. Wannan taron wani muhimmin taro ne a duk faɗin Nijeriya a ɓangaren fasaha tare da ƙarfafa guiwar matasa wajen cikar muradan su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Taliya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Dr Ali Larijan wanda ya ke ziyarar aiki na kwanaki uku a kasar Pakistan ya yabawa kasar saboda goyon bayan da ta bawa kasarsa a lokacin yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka dorawa kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Dr Ali Larijana yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Talata. Sannan yace ya isar da sakon gaisuwa na Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khami’ae ga mutanen kasar Pakistan. Banda haka ya gana da Firai ministan kasar Shehbaz Sharif da shugaban kasa Asif Ali Zardari da kuma kakakin majalisar dokokin kasar kasar Sardar Avaz Saadik.
A ganawar Larijani da Sharif sun tattauna kan dangantaka mai tsawo da ke tsakanin Iran da Pakisatan, da kuma bukatar a kara zurfafata.
Sharif a nasa bangaren ya bayyana cewa nan ba da dadewa waministan harkokin wajen kasar Mohammad Ishak Dar zai ziyarci Tehran inda ake saran zai rattaba hannu kan yarjeniyoyi na bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu, daga ciki har da batun kammala aikin shimfida bututun gas daga kasar Iran zuwa Pakistan. Da kuma harkokin sadarwa.
A cikin wannan shekarar ne dai kasashen biyu suka rattaba hannu kan yarjeniyar bunkasa kasuwanci ta dalar Amurka billion 10 a tsakaninsu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah November 26, 2025 UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin Lebanon November 26, 2025 Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru Mafaka Ta Wucin Gadi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci