Gwamnatin Tarayya za ta fara farautar masu takardun bogi a wajen aiki a wat
Published: 25th, September 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta umarci dukkanin ma’aikatu, hukumomi, sojoji da kuma cibiyoyin kuɗi da ma’aikatu masu zaman kansu da su fara tantance takardun shaidar kammala makaranta na ma’aikatansu daga ranar 6 ga watan Oktoba, 2025.
Wannan mataki ya biyo bayan yawaitar bogi da takardun karatu na bogi a Najeriya.
Za a yi tantancewar ne ta hanyar tsarin amfani da kwamfuta mai suna Nigeria Education Repository and Databank (NERD), wanda aka ƙirƙiro domin adanawa da tabbatar da sahihancin takardun karatun ma’aikata.
A wannan tsari, babu wanda za a ɗauka aiki ko a tabbatar masa da muƙami sai an tabbatar da takardunsa ta hanyar National Credential Verification Service (NCVS).
Kowace takarda da aka tabbatar za a ba ta wata lamba ta musamman mai tsaro.
Jami’ai sun ce wannan mataki zai kare mutuncin ilimi a Najeriya, kodayake masana sun yi gargaɗin cewa wasu za su iya rasa ayyukansu.
A baya, an gano ’yan Najeriya da dama suna amfani da takardun bogi don samun aiki ko ƙarin matsayi a wajen aiki.
A shekarar 2024, gwamnati ta soke takardun shaidar kammala karatu sama da 22,000 daga jami’o’in bogi na Jamhuriyar Benin da Togo.
Haka kuma, gwamnati ta umarci cibiyoyi su riƙa gabatar da rahoton bin doka duk shekara domin tabbatar da tsauraran matakai.
Wannan zai sa ya zama da wuya a riƙa yin amfani da takardun ƙarya ba tare da an gano su ba.
Masana ilimi sun ce idan aka aiwatar da tsarin yadda ya kamata, zai dawo da mutuncin takardun shaidar kammala karatu na Najeriya a idon duniya, tare da bai wa ɗalibai na gari damar samun aiki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Takardun bogi Takardun Shaidar Kammala Karatu Tantancewa da takardun
এছাড়াও পড়ুন:
Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, a ranar Litinin ya ziyarci ɗaliban jihar da ke karatu a ƙasar Indiya, inda ya ba kowannen su tallafin Naira 500,000.
Gwamnan, wanda ke ziyarar aiki a Indiya, ya fara ganawa da waɗanda suka ci gajiyar shirin tallafin karatu na jihar a Jami’ar Sharda da ke Noida.
Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kaiYa tabbatar musu da jajircewar gwamnatinsa wajen kula da walwalarsu domin samun nasarar karatunsu, sannan ya gargade su da su mai da hankali kan karatun nasu.
Ya ce, “Na zo nan yau saboda dalili ɗaya, don tunatar da ku cewa gwamnatin Jihar Borno na alfahari da ku, wadda kan haka take saka hannun jari a kan makomarku.
“Kuna da muhimmanci ga ci gaba da sake gina jiharmu. Ilimin da ƙwarewar da kuke samu a nan zai amfani, ga jama’arku da kuma kannenku masu zuwa,” in ji Zulum.
Gwamna Zulum ya bayar da tallafin kuɗi na Naira 500,000 ga kowane ɗalibi, abin da ya jawo farin ciki matuƙa ga ɗaliban.
Daga nan, gwamnan ya tafi zuwa yankin Lucknow a ƙasar Indiya, inda ya yi irin wannan taimako ga ɗaliban Jihar Borno a Jami’ar Integral.
Ya kuma ba da umarni a bai wa waɗanda suka ci gajiyar tallafin karatu na Jihar Borno da ke karatu a ƙasar Malesiya irin wannan tallafin kuɗi, yana mai jaddada alkawarin yin adalci ga dukkan ɗaliban da ke amfana da shirin tallafin karatu.
Ɗaliban sun yaba wa gwamnan saboda ziyarar, inda bayyana shi a matsayin shugaba mai tausayi da kulawa.
A cikin tawagar gwamnan akwai Babban Sakataren Fadar Gwamnatin Borno, Barista Mustapha Busuguma da Babban Sakataren Hukumar BOGIS, Injiniya Adam Bukar Bababe.