Shugaban EFCC ya bayyana a Aso Rock yayin da Tinubu ya gana da Ibas
Published: 25th, September 2025 GMT
Shugaban Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), Ola Olukoyede, ya bayyana a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, yayin da Shugaba Bola Tinubu, ya gana da tsohon shugaban riƙo na Jihar Ribas, Vice Admiral Ibok Ete Ibas (mai ritaya).
Ya fadar ne a daidai lokacin da Shugaba Tinubu ya gana da Ibas.
Tinubu, ya naɗa Ibas a watan Maris domin jagorantar jihar bayan rikicin siyasa da ya ɓarke tsakanin tsohon gwamna Nyesom Wike da wanda ya gaje shi, Siminalayi Fubara.
Domin shawo kan rikicin, Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a ranar 18 ga watan Maris, inda aka dakatar da Fubara, mataimakiyarsa da ’yan majalisar dokokin jihar.
Majalisar Dattawa da ta Wakilai sun goyi bayan matakin a ranar 20 ga watan Maris.
Ibas, ya bar ofis a makon da ya gabata, yayin da Fubara da sauran masu muƙamai suka koma kan kujerunsu.
Sai dai wasu sun zargi Ibas da rashin kawo ci gaba a lokacin da ya jagoranci jihar na tsawon watanni shida.
Majalisar Dokokin Jihar Ribas, ta ce za ta binciki yadda ya kashe kuɗaɗen jihar a lokacin dokar ta-ɓaci.
Rahotanni sun nuna cewa jihar ta samu kusan Naira biliyan 254.37 daga asusun ƙasa daga tsakanin watan Maris zuwa Agustan 2025.
Haka kuma, an hangi Ministan Kuɗi, Wale Edun, a fadar shugaban ƙasa.
Sai dai babu tabbacin ko zuwan Olukoyede da Edun, na da nasaba da batun Jihar Ribas.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fadar Shugaban Ƙasa Fubara Ganawa Siyasa watan Maris
এছাড়াও পড়ুন:
Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe
Majiyar ‘yan hamayyar siyasar kasar Uganda sun sanar da cewa, jami’an tsaron kasar sun kama magoya bayan Bobi Wine dake takarar shugabancin kasar 300 a tsawon yakin neman zabe.
Mai magana da yawun Bobi Wine dan takarar shugabancin kasar ya fada a jiya Talata cewa; jami’an tsaron kasar sun kama fiye da mutane 300 da suke goyon bayansa tun da aka fara yakin neman zabe daga watan Janairu zuwa yanzu.
Bob Wine wanda shahararren mawaki ne ya juye zuwa dan siyasa, yana yin takara a karo na biyu da shugaban kasar mai ci, Uweri Musaveni. A zaben 2021 Bob Wine wanda sunansa na yanke shi ne Robert Kyagulanyi,, ya zo na biyu.
Kakakin jam’iyyarsa ta NUP,ya ce, a cikin wannan makon ma an kama mutane da dama, kuma ana tsare da su ne a cikin babban birnin kasar Kamfala.
Majiyar jam’iyyar hamayyar ta kuma ce, a ranar Litinin da aka bude yakin neman zabe kadai na kame mutane sun kai 100, sai kuma wani adadi mai yawa a jiya Talata.
Jami’an tsaron kasar sun sanar da kame mutane 7 bayan da su ka yi jefe-jefe da duwatsu a lokacin yakin neman zabe.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta November 26, 2025 Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki November 26, 2025 Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin November 26, 2025 Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah November 26, 2025 UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin Lebanon November 26, 2025 Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci