Gwamnatin Jihar Jigawa tace tana gudanar da ayyukan gyara da ginawa da kuma inganta hanyoyin mota domin cimma kudirin ta na bunkasa bangaren aikin noma.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka yayin kaddamar da aikin sanya kwalta akan hanyar Dandi da Farin Daba zuwa Gada a karamar hukumar Kazaure.

Ya ce gwamnatin jihar ta bada kwangilar aikin ne akan kudi sama da Naira miliyan dubu 8 da miliyan 200 tare da wa’adin kammala aiki a watanni 18.

Kazalika, Malam Umar Namadi ya kuma bude aikin gina hanyar Farin Daba, Galo Babba zuwa Galo Karama da aka ba da kwangilar su kan naira miliyan dubu shida da miliyan 300.

Ya kara da cewar, aikin zai saukaka wa manoma kai kayan amfanin gonar su zuwa kasuwanni.

A don haka, Namadi ya tabbatar wa jama’ar jihar cewar gwamnatin sa na da burin samar musu da abubuwan more rayuwa.

A jawabin sa, Kwamishinan Ayyuka da Sufuri na jihar, Injiniya Gambo S. Malam, yace aikin Dandi-Farin Daba-Gada an ba da shi ne ga wasu kamfanoni guda 2 tare da wa’adin kammalawa cikin watanni 24.

Injiniya Gambo ya kara da cewar, za a yi wasu ayyuka kamar gina magudanan ruwa da cika gefen hanya da sauran su.

Taron bude aikin ya samu halartar Mataimakin Gwamna Injiniya Aminu Usman, Ministar Ilimi, Farfesa Suwaiba Said Ahmed, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Alhaji Haruna Aliyu Dangyatum da sauran mambobin majalisar zartaswa ta jihar.

 

Usman Mohammed Zaria

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, a ranar Litinin ya ziyarci ɗaliban jihar da ke karatu a ƙasar Indiya, inda ya ba kowannen su tallafin Naira 500,000.

Gwamnan, wanda ke ziyarar aiki a Indiya, ya fara ganawa da waɗanda suka ci gajiyar shirin tallafin karatu na jihar a Jami’ar Sharda da ke Noida.

Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai

Ya tabbatar musu da jajircewar gwamnatinsa wajen kula da walwalarsu domin samun nasarar karatunsu, sannan ya gargade su da su mai da hankali kan karatun nasu.

Ya ce, “Na zo nan yau saboda dalili ɗaya, don tunatar da ku cewa gwamnatin Jihar Borno na alfahari da ku, wadda kan haka take saka hannun jari a kan makomarku.

“Kuna da muhimmanci ga ci gaba da sake gina jiharmu. Ilimin da ƙwarewar da kuke samu a nan zai amfani, ga jama’arku da kuma kannenku masu zuwa,” in ji Zulum.

Gwamna Zulum ya bayar da tallafin kuɗi na Naira 500,000 ga kowane ɗalibi, abin da ya jawo farin ciki matuƙa ga ɗaliban.

Daga nan, gwamnan ya tafi zuwa yankin Lucknow a ƙasar Indiya, inda ya yi irin wannan taimako ga ɗaliban Jihar Borno a Jami’ar Integral.

Ya kuma ba da umarni a bai wa waɗanda suka ci gajiyar tallafin karatu na Jihar Borno da ke karatu a ƙasar Malesiya irin wannan tallafin kuɗi, yana mai jaddada alkawarin yin adalci ga dukkan ɗaliban da ke amfana da shirin tallafin karatu.

Ɗaliban sun yaba wa gwamnan saboda ziyarar, inda bayyana shi a matsayin shugaba mai tausayi da kulawa.

A cikin tawagar gwamnan akwai Babban Sakataren Fadar Gwamnatin Borno, Barista Mustapha Busuguma da Babban Sakataren Hukumar BOGIS, Injiniya Adam Bukar Bababe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa
  • Mali: An Dakatar Da  Aikin Kafafen Watsa Labarun Faransa Biyu A Cikin Kasar Mali
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja