Aminiya:
2025-10-13@15:49:50 GMT

Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar rasuwar Sarkin Zuru

Published: 17th, August 2025 GMT

Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, ta bayyana alhininta game da rasuwar Sarkin Zuru na Jihar Kebbi, Mai Martaba Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (mai ritaya) Gomo II, wanda ya rasu yana da shekaru 81.

Shugaban ƙungiyar, Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce marigayin jagora ne mai kishin ƙasa, dattijo nagari kuma basarake mai daraja wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa Najeriya hidima.

Ta’aziyyar Sarkin Zuru: Muhammadu Sani Sami (1943-2025) Adam A. Zango ya auri jarumar Kannywood

A cikin sanarwar ta’aziyyar da mai magana da yawunsa, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar, gwamnan ya tuna irin rawar da Sarkin ya taka a aikin soja.

Ya ce Sarkin ya taka rawa sosai lokacin da ya yi Gwamnan soja na tsohuwar Jihar Bauchi, inda ya bayar da gudunmawa wajen ci gaban jihar.

Ya kuma bayyana yadda marigayin ya yi ƙoƙarin wajen ci gaban masarautar Zuru da kuma ƙarfafa majalisar sarakunan gargajiya ta Arewa.

Ƙungiyar ta miƙa ta’aziyyarta ga iyalan marigayin, masarautar Zuru da al’ummar Jihar Kebbi.

Ta kuma roƙi Allah Ya jikansa, Ya kuma gafarta masa, Ya kuma sanya Aljannatul Firdaus ta zama makomarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnoni Arewa Ƙungiya rasuwa Sarkin Zuru ta aziyya

এছাড়াও পড়ুন:

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025 Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi October 10, 2025 Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC  October 9, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar .
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • ’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi 
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya