Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar rasuwar Sarkin Zuru
Published: 17th, August 2025 GMT
Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, ta bayyana alhininta game da rasuwar Sarkin Zuru na Jihar Kebbi, Mai Martaba Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (mai ritaya) Gomo II, wanda ya rasu yana da shekaru 81.
Shugaban ƙungiyar, Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce marigayin jagora ne mai kishin ƙasa, dattijo nagari kuma basarake mai daraja wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa Najeriya hidima.
A cikin sanarwar ta’aziyyar da mai magana da yawunsa, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar, gwamnan ya tuna irin rawar da Sarkin ya taka a aikin soja.
Ya ce Sarkin ya taka rawa sosai lokacin da ya yi Gwamnan soja na tsohuwar Jihar Bauchi, inda ya bayar da gudunmawa wajen ci gaban jihar.
Ya kuma bayyana yadda marigayin ya yi ƙoƙarin wajen ci gaban masarautar Zuru da kuma ƙarfafa majalisar sarakunan gargajiya ta Arewa.
Ƙungiyar ta miƙa ta’aziyyarta ga iyalan marigayin, masarautar Zuru da al’ummar Jihar Kebbi.
Ta kuma roƙi Allah Ya jikansa, Ya kuma gafarta masa, Ya kuma sanya Aljannatul Firdaus ta zama makomarsa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnoni Arewa Ƙungiya rasuwa Sarkin Zuru ta aziyya
এছাড়াও পড়ুন:
Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025
Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi October 10, 2025
Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC October 9, 2025