Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako
Published: 13th, October 2025 GMT
Gidajen mai da dam aka rufe, yayin da wadanda suka kasance da dan sauran mai kuma, layuka ne marasa iyaka suka makare su, lamarin da ta kai har kwana mutane ke yi a gidajen man.
A kan titunan babban birnin kasar, bayanai sun ce ba kasafai ake ganin motoci suna kai komo ba, ko kuma mutane na tura babura, bisa alama dai mutane sun ajiye ababen hawansu a gida.
Sai dai duk da wannan karancin man da ake fama da shi, farashinsa ya ci gaba da kasancewa a yanda yake, domin kuwa farashin lita na mai CFA 775 yayin da dizal yake akan CFA 725.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
Sufeton ƴansanda na Ƙasa, IGP Kayode Egbetokun, ya maye gurbin Kwamishinan ƴansandan birnin tarayya, CP Ajao Adewale, sakamakon ƙaruwar matsalolin tsaro a Abuja. Wannan mataki ya biyo bayan matsin lamba da yake fuskanta saboda rashin gamsuwa da aikinsa tun bayan karɓar ragama daga CP Benneth Igwe.
Majiyoyi daga cikin rundunar sun bayyana cewa sauya shi ya shafi yadda matsalolin tsaro ke ƙaruwa a Abuja, musamman bayan harin fashi da makami da ya yi sanadin mutuwar mai gabatar da shirye-shiryen gidan talabijin ɗin ARISE, Somtochukwu Maduagwu, da mai gadi Barnabas Danlami, a Katampe, ranar 29 ga Satumba, 2025.
Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A AbujaWata wasiƙar cikin gida daga shalƙwatar ƴansanda ta tabbatar da cewa CP Miller Gajere Dantawaye ne aka naɗa sabon kwamishinan ƴansanda na FCT, yayin da DCP Wilson Aniefiok Akpan aka tura shi zuwa jihar Kogi.
Wasiƙar, mai lamba TH.5361/FS/FHQ/ABJ/SUB.6/213, ta bayyana cewa wannan sauyin na ɗan lokaci ne har sai hukumar aiyukan ƴansanda ta ƙasa (PSC) ta amince da cikakken naɗin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA