An tafka asara bayan gobara ta ƙone Kwalejin Sheikh Dahiru Bauchi
Published: 18th, May 2025 GMT
Gobara ta tashi a Kwalejin Karatun Alƙur’ani da ilimin addinin Musulunci mallakin fitaccen malamin nan, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, da ke Rafin Albasa, a Jihar Bauchi, inda ta ƙone ginin makarantar da kayan cikinta.
Binciken wakilinmu ya gano cewa gobarar ta lalata bene mai ɗakuna da dama ciki har da ofisoshi, ajujuwa, ɗakunan gwaje-gwaje, ɗakunan kwamfuta, da ɗakunan karatu.
An kuma rasa kayan sawa na malamai da ɗalibai, katifu, barguna da sauran kayayyakin amfanin yau da kullum.
Har yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar ba.
Sai dai daraktan makarantar, Sayyadi Aliyu Sise Dahiru, ya ce sun gode wa Allah da ba a rasa rai ko samun rauni ba.
“Lamarin ya faru ne bayan an kammala karatu da yamma, kuma muna godiya ga jami’an kashe gobara da suka kwashe sa’o’i suna ƙoƙarin kashe wutar,” in ji shi.
Ya ce makarantar na da alaƙa da Jami’ar Azhar da ke ƙasar Masar, kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Namadi Sambo ne ya ƙaddamar da ita.
A cewarsa, makarantar kwana ce da ke bayar da ilimin boko da na Islamiyya tare da koyar da sana’o’i.
Kowace shekara ana yaye mahaddatan Alƙur’ani da dama a makarantar.
Ya ce an rasa litattafan Sheikh Dahiru Bauchi da na sauran malamai da dama, ciki har da kwamfutoci da kayan aikin makaranta.
Hukumar kashe gobara ta Jihar Bauchi ta bayyana cewa gobarar ta ƙone littattafai kusan 7,228, suturar ɗalibai kusan 583, gadaje 250, darduma mai faɗin mita 355, kujerun cin abinci 324, katifu, jakunkuna, kayan girki da sauran muhimman takardu da hotuna guda 150.
Ana ci gaba da bincike don gano musabbabin tashin gobarar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai Gobara Kayan Karatu
এছাড়াও পড়ুন:
Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa Maryam Sanda afuwa, wadda aka yanke wa hukuncin kisa a shekarar 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, ɗan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Alhaji Haliru Bello.
Maryam,’ mai shekara 37, ta shafe shekaru shida da watanni takwas a gidan yarin Suleja kafin yi mata afuwa.
Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaroRahotanni sun nuna cewar an yi mata afuwar ne bayan yin nadama da aikata kyakkyawan halaye.
Iyayen Maryam sun roƙi gwamnati da ta sake ta saboda ’ya’yanta biyu da ta ke da alhakin kula da su, tare da alƙawarin sauya halayenta.
Shugaba Tinubu, ya kuma yi wa wasu mutane afuwa da suka haɗa da Manjo Janar Mamman Vatsa, Ken Saro-Wiwa, da kuma Sir Herbert Macaulay.
Gaba ɗaya mutane 175 ne shugaban ya yi musu afuwa, ciki har da masu manyan laifuka, tsoffin fursunoni, da waɗanda suka yi kyakkyawan tuba.
Wannan shi ne karon farko da Shugaba Tinubu ya yi amfani da ikon yafe laifi don tausaya wa waɗanda suka aikata laifuka tun bayan hawansa mulki.