Aminiya:
2025-05-18@23:16:15 GMT

An tafka asara bayan gobara ta ƙone Kwalejin Sheikh Dahiru Bauchi

Published: 18th, May 2025 GMT

Gobara ta tashi a Kwalejin Karatun Alƙur’ani da ilimin addinin Musulunci mallakin fitaccen malamin nan, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, da ke Rafin Albasa, a Jihar Bauchi, inda ta ƙone ginin makarantar da kayan cikinta.

Binciken wakilinmu ya gano cewa gobarar ta lalata bene mai ɗakuna da dama ciki har da ofisoshi, ajujuwa, ɗakunan gwaje-gwaje, ɗakunan kwamfuta, da ɗakunan karatu.

Jami’in Sibil Difens ya mayar da N800,000 da wata Hajiya ta zubar a Adamawa Yadda ’ya’yan shugabanni ke musu yaƙi da ’yan adawa

An kuma rasa kayan sawa na malamai da ɗalibai, katifu, barguna da sauran kayayyakin amfanin yau da kullum.

Har yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar ba.

Sai dai daraktan makarantar, Sayyadi Aliyu Sise Dahiru, ya ce sun gode wa Allah da ba a rasa rai ko samun rauni ba.

“Lamarin ya faru ne bayan an kammala karatu da yamma, kuma muna godiya ga jami’an kashe gobara da suka kwashe sa’o’i suna ƙoƙarin kashe wutar,” in ji shi.

Ya ce makarantar na da alaƙa da Jami’ar Azhar da ke ƙasar Masar, kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Namadi Sambo ne ya ƙaddamar da ita.

A cewarsa, makarantar kwana ce da ke bayar da ilimin boko da na Islamiyya tare da koyar da sana’o’i.

Kowace shekara ana yaye mahaddatan Alƙur’ani da dama a makarantar.

Ya ce an rasa litattafan Sheikh Dahiru Bauchi da na sauran malamai da dama, ciki har da kwamfutoci da kayan aikin makaranta.

Hukumar kashe gobara ta Jihar Bauchi ta bayyana cewa gobarar ta ƙone littattafai kusan 7,228, suturar ɗalibai kusan 583, gadaje 250, darduma mai faɗin mita 355, kujerun cin abinci 324, katifu, jakunkuna, kayan girki da sauran muhimman takardu da hotuna guda 150.

Ana ci gaba da bincike don gano musabbabin tashin gobarar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai Gobara Kayan Karatu

এছাড়াও পড়ুন:

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Kwanan nan ne Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da rahoton dake sabunta hasashen yanayin tattalin arzikin duniya gami da makomarsa na shekara ta 2025 a tsakiyar shekarar da muke ciki, inda rahoton ke ganin kara harajin kwastam da rashin sanin tabbas game da manufofin cinikayya sun janyo tabarbarewar makomar tattalin arzikin duk duniya, tare da haifar da tarin kalubaloli ga kasa da kasa, musamman kasashe masu tasowa, ciki har da kasar Sin.

Rahoton na hasashen cewa, saurin karuwar tattalin arzikin duniya na bana, zai ragu zuwa kaso 2.4 bisa dari, yayin da saurin karuwar cinikayya zai ragu zuwa kaso 1.6 bisa dari. Kana, rahoton na ganin cewa, daidaita manufofi gami da hadin-gwiwar kasa da kasa, na da muhimmanci gaya ga samar da ci gaba ga tattalin arzikin duniya, da tabbatar da dorewarsa.

Game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana a jiya Jumma’a cewa, abubuwa na zahiri sun shaida cewa, dunkulewar tattalin arzikin duniya baki daya muhimmin abu ne da kowa zai amince da shi, kuma bude kofa ga kowa da inganta hadin-gwiwa muhimmin abu ne da ya kamata mu yi a wannan zamanin da muke ciki, kazalika, ra’ayin cudanyar bangarori daban-daban shi ne zabin da ya zama dole.

Kakakin ya kuma jaddada cewa, har kullum kasar Sin na tsayawa ga fadada bude kofarta ga kasashen waje, kuma bude kofar kasar Sin, dama ce ga duk duniya har abada. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)
  • Motar da aka shekara 10 ana tara kuɗinta ta ƙone bayan awa 1 da sayen ta
  • An yi zanga-zanga zagayowar ranar ‘’Nakba’’ a sassan duniya da dama
  • Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 
  • Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas
  • Iran: Cikakken Goyon Bayan Amurka Ga ‘Yan Sahayoniya Ne Yake Sa Su Tafka Laifuka
  • Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci