Shugaban kasar Iran ya jaddadacewa: Sun yi Imani da tattaunawa, amma ba su jin tsoron duk wata barazana

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa: Tabbas Iran tana gudanar da zaman tattaunawa da Amurka amma ba ta tsoron duk wata barazanarta, yana mai nuni da kalaman Trump da ke cin karo da juna, wani lokaci yana magana kan zaman lafiya sannan a wasu lokutan yana barazana da yaki.

A jawabin da ya gabatar a wajen bikin cika shekaru biyu da samun nasarar tawagar “Rukunin Jirgin Ruwa na 86” na sojojin ruwan Iran, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yaba da sadaukarwar da jaruman da suka yi wannan hidimar, yana mai cewa: “Suna alfahari da kasancewar dakarunsu, yana mai jaddada cewa; Ya ku masoya, hangen nesa na sojojin ruwa da dukkanin masu kare wannan kasa mai tsarki suke dauke da shi abin alfahari ne a gare kasar Iran.”

Ya kara da cewa: A kodayaushe ya yi imanin cewa: Iran ba za ta amince da kasance kasa da sauran kasashe a kowane fanni ba. Nasarorin da Iran ta samu wajen samar da jiragen ruwa na karkashin ruwa, masu dauke manyan makamai masu tarwatsa jirgi, da makamai da aka kera a cikin gida, ba tare da dogaro da bangarorin ketare ba, da mayar da Iran ta zama mai fitar da kayan soja zuwa kasashen waje, abin alfahari ne.

Shugaban ya yi gargadi kan yunkurin makiya na yada dabi’ar nuna gajiyawa a tsakanin al’ummar Iran, da haifar da sabani a tsakanin jami’ai, yana mai cewa: A karkashin jagorancin Jagoran juyin juya halin Musulunci, hadin kai ya fi karfi a yau fiye da kowane lokaci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

 

A nasa tsokaci kuwa, sakataren gwamnatin Mozambique mai kula da ma’adinai Jorge Daudo, cewa ya yi lardin Shandong yana daya daga cikin larduna masu kwazo da ci gaban masana’antu a Sin, kuma yana da karfi a fannonin hakar ma’adinai, da sarrafa karafa da masana’antu. Sabo da haka, Mozambique na fatan kara yin hadin gwiwa da lardin na Shandong. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia October 11, 2025 Daga Birnin Sin Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa October 11, 2025 Daga Birnin Sin Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
  • Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi
  • Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)
  • Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon
  • An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa
  • Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya