Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Ce Ba Ta Tsoron Duk Wata Barazana Don Neman Tauyaye Mata Hakki
Published: 17th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya jaddadacewa: Sun yi Imani da tattaunawa, amma ba su jin tsoron duk wata barazana
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa: Tabbas Iran tana gudanar da zaman tattaunawa da Amurka amma ba ta tsoron duk wata barazanarta, yana mai nuni da kalaman Trump da ke cin karo da juna, wani lokaci yana magana kan zaman lafiya sannan a wasu lokutan yana barazana da yaki.
A jawabin da ya gabatar a wajen bikin cika shekaru biyu da samun nasarar tawagar “Rukunin Jirgin Ruwa na 86” na sojojin ruwan Iran, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yaba da sadaukarwar da jaruman da suka yi wannan hidimar, yana mai cewa: “Suna alfahari da kasancewar dakarunsu, yana mai jaddada cewa; Ya ku masoya, hangen nesa na sojojin ruwa da dukkanin masu kare wannan kasa mai tsarki suke dauke da shi abin alfahari ne a gare kasar Iran.”
Ya kara da cewa: A kodayaushe ya yi imanin cewa: Iran ba za ta amince da kasance kasa da sauran kasashe a kowane fanni ba. Nasarorin da Iran ta samu wajen samar da jiragen ruwa na karkashin ruwa, masu dauke manyan makamai masu tarwatsa jirgi, da makamai da aka kera a cikin gida, ba tare da dogaro da bangarorin ketare ba, da mayar da Iran ta zama mai fitar da kayan soja zuwa kasashen waje, abin alfahari ne.
Shugaban ya yi gargadi kan yunkurin makiya na yada dabi’ar nuna gajiyawa a tsakanin al’ummar Iran, da haifar da sabani a tsakanin jami’ai, yana mai cewa: A karkashin jagorancin Jagoran juyin juya halin Musulunci, hadin kai ya fi karfi a yau fiye da kowane lokaci.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Larijani a Beirut: Iran A Shirye take ta taimaka ma Lebanon
Shugaban majalisar dokokin kasar Lebanon Nabih Berri ya tarbi Ali Larijani, sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran a hedikwatar shugaban kasa ta biyu dake Ain al-Tineh. Larijani ya tabbatar da cewa bayan ganawar da aka yi tsakanin kasashen Labanon da Iran lamarin ya yi kyau da armashi.
Ya jaddada cewa Iran ba ta da niyyar yin katsalandan a cikin harkokin cikin gidan kasar Labanon, yana mai cewa bai kamata wasu kasashe su ba da umarni ga gwamnatin Lebanonba, musamman kan wasu batutuwa masu sarkakiya wadanda al’ummar Lebanon ne tare da gwamnatinsu kawai za su iya yanke shawarar a kansu.
Larijani ya jaddada cewa Iran ba ta zo da wani shiri a Labanon ba, sai dai Amurkawa sun zo ne da takardarsu da ke neman jefa Kasara cikin yamutsi.
Larijani ya jaddada cewa Iran na mutunta duk wani matakin da gwamnati za ta dauka tare da hadin gwiwa da sauran bangarori daban-daban na kasar Lebanon.
Kafin nan Larijani ya gana da shugaba Joseph Aoun a babbar fadar shugaban kasa da ke Baabda.
A wata sanarwa da fadar shugaban kasar Labanon ta fitar bayan ganawar ta bayyana cewa, Larijani ya sake sabunta gaisuwar shugaban kasar Iran ga shugaba Aoun tare da gayyatarsa zuwa birnin Tehran, inda ya kara da cewa “Larijani ya tabbatar da cewa Iran a shirye take ta taimaka wa kasar Lebanon idan har gwamnatin Lebanon tana bukatar hakan so”, inda Aoun ya sanar da Larijani cewa “sha’awar kasar Lebanon na yin hadin gwiwa da kasar Iran a kan dangantakar da ke tsakaninta da Iran abu ne tabbatace.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Masar ta yi Allawadai da ikirarin Netanyahu game shirinsa na kafa Isra’ila Babba August 14, 2025 Hamas ta aike da wasikar yabo ga Yemen kan goyon bayan Gaza August 14, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 130 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 129 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 128 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 127 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 126 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 125 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 124 August 13, 2025 Iran: Babu Mika Kai Ga Takurawar kasashen Yamma har sai An Kawo Karshen Barazana August 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci