Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
Published: 16th, May 2025 GMT
Mai magana da yawun ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin, He Yongqian, ta bayyana a yau Alhamis cewa, kasar Sin ta bukaci Amurka ta dakatar da matakan kakaba harajin da ta dauka bisa binciken sashe na 232 ba tare da wani bata lokaci ba.
A yayin taron manema labaru na yau da kullum, jami’ar ta ce, harajin kwastam na sashe na 232 da aka kakaba wa motocin da ake shigar da su daga waje, da karafa, da holoko, da kuma binciken sashe na 232 kan magunguna, “zallar aiki ne na mamayar bangare daya da kuma kariyar cinikayya.
Jami’ar ta kara da cewa, kasar Sin ta yi kira ga Amurka da ta gaggauta kawo karshen matakan harajin na sashe na 232, tare da magance korafe-korafen dukkan bangarori yadda ya kamata, ta hanyar tattaunawa bisa daidaito. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi Uwargida Oluremi Tinubu wacce ta ba da Naira miliyan 110 ga iyalan marigaya.
An kuma yi alƙawarin cewa gwamnati za ta ɗauki nauyin ilimin yaran waɗanda suka rasu da kuma taimaka wa matansu da iyayensu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp