An kama wata mata kan zargin safarar makamai zuwa Katsina
Published: 15th, May 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wata mata mai shekara 21 mai suna Fatima Salisu da ake zargi da safarar makamai, biyo bayan samun bayanan sirri.
Kakakin rundunar ’yan sanda, Ramhan Nansel ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis.
Ganduje ya halarci Majalisar Wakilai don sheda ’Yan Majalisa 2 zuwa APC Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a FilatoKakakin ya ce an kama Fatima ne da laifin safarar alburusai ta yankin Keana da Doma a cikin Jihar Nasarawa don taimakon masu aikata laifuka a Katsina, inda take zaune.
“Cikin gaggawa kan bayanan sirri da aka samu, Kwamishinan ’yan sanda CP Shetima J. Mohammed, ya ba da umarnin tura sashin yaƙi da masu garkuwa da mutane na rundunar cikin gaggawa.
“Tawagar ta yi aiki tuƙuru, wanda ya kai ga kama wanda ake zargin tare da ƙwato alburusai 400 ƙirar 7.62ɗ39mm da harsashi 81 na 7.62mm na NATO.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “A yanzu haka ana tsare da wanda ake zargin kuma ana yi mata tambayoyi mai tsanani yayin da masu bincike ke ƙoƙarin tarwatsa cibiyar safarar makamai da kuma gano alaƙarta da ’yan fashi da makami da ta’addanci.”
Nansel ya bayyana cewa, kama matar yana wakiltar wani babban ci gaba a yaƙi da safarar makamai da aikata laifuka a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Nasarawa safarar makamai
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja
Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja, ya yaba wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan kama Abubakar Abba, jagoran kungiyar Mahmuda, daya daga cikin manyan kungiyoyin ta’addanci da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta yi a Najeriya.
An ce an kama shi ne a Wawa da ke karamar hukumar Borgu ta Jihar Neja inda aka kai shi Abuja domin ci gaba da bincike.
Gwamna Umar Bago ya bayyana matakin a matsayin nuni da irin jajircewar da shugaba Bola Ahmed Tinubu ke yi na tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan Nijeriya.
Gwamnan wanda ya yi magana ta bakin babban sakataren yada labaran sa, Bologi Ibrahim, ya ce, “Eh gaskiya ne, zan iya tabbatar da cewa hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta kama shugaban kungiyar Mahmuda da ke daya daga cikin kungiyoyin ta’addanci a yammacin Afirka, Abubakar Abba, wanda jami’an tsaron farin kaya DSS suka kama shi da ransa.
“Wannan babbar nasara ce a gare mu a matsayinmu na jama’a da kuma gwamnati, kuma Shugaba Tinubu ya cancanci a yaba masa kan wannan labari mai ban sha’awa, yana mai jaddada cewa “Kamun Abba ya nuna cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jajirce wajen kawo karshen rashin tsaro da kuma inganta rayuwar ‘yan Nijeriya. In ji Gwamna Bago.
Gwamnan ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar Neja za ta ci gaba da hada kai da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro domin ganin an dakile ta’addanci a jihar Neja da Najeriya.
ALIYU LAWAL.