Aminiya:
2025-06-18@02:45:29 GMT

An kama wata mata kan zargin safarar makamai zuwa Katsina

Published: 15th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wata mata mai shekara 21 mai suna Fatima Salisu da ake zargi da safarar makamai, biyo bayan samun bayanan sirri.

Kakakin rundunar ’yan sanda, Ramhan Nansel ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis.

Ganduje ya halarci Majalisar Wakilai don sheda ’Yan Majalisa 2 zuwa APC Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato

Kakakin ya ce an kama Fatima ne da laifin safarar alburusai ta yankin Keana da Doma a cikin Jihar Nasarawa don taimakon masu aikata laifuka a Katsina, inda take zaune.

“Cikin gaggawa kan bayanan sirri da aka samu, Kwamishinan ’yan sanda CP Shetima J. Mohammed, ya ba da umarnin tura sashin yaƙi da masu garkuwa da mutane na rundunar cikin gaggawa.

“Tawagar ta yi aiki tuƙuru, wanda ya kai ga kama wanda ake zargin tare da ƙwato alburusai 400 ƙirar 7.62ɗ39mm da harsashi 81 na 7.62mm na NATO.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “A yanzu haka ana tsare da wanda ake zargin kuma ana yi mata tambayoyi mai tsanani yayin da masu bincike ke ƙoƙarin tarwatsa cibiyar safarar makamai da kuma gano alaƙarta da ’yan fashi da makami da ta’addanci.”

Nansel ya bayyana cewa, kama matar yana wakiltar wani babban ci gaba a yaƙi da safarar makamai da aikata laifuka a yankin.

 

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nasarawa safarar makamai

এছাড়াও পড়ুন:

An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran

Isra’ila ta tabbatar cewa an garzaya da ’yan ƙasarta aƙalla 154 asibiti bayan sabbin hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kawo mata.

Ma’aikatar lafiyar Isra’ila ta ce aƙalla mutum huɗu daga cikin waɗanda aka kai asibitin suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai, wasu biyar kuma na samun kulawa ta musamman saboda tsananin tashin hankali.

Alkaluman da ma’aikatar ta fitar sun nuna cewa mutum 130 daga cikin majinyatan sun samu raunuka marasa tsanani a sakamakon hare-haren.

Wannnan na zuwa ne a yayin da Iran ta ci gaba luguden rokoki a matsayin ramuwar gayya a sassan Isra’ila a a ranar Talata.

Isra’ila ta ce Iran ta lashe mata mutane akalla 24.

A ɗaya ɓangaren kuma Iran cewa harin tsokana da Isra’ila ta kai mata ya yi ajalin kimanin mutum 224.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi
  • Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
  • An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran
  • Iran ta rataye mutumin da ta kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri
  • Dan Asalin Tudun Loess
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina
  • Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila