’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya
Published: 15th, May 2025 GMT
A ranar Talata ma, an sake kai hari a ƙauyen Kungurki.
Jaji, wanda ya taɓa zama Shugaban Kwamitin Tsaro da Leƙen Asiri a Majalisar Wakilai ta 8, ya ce bai dace a ayyana dokar ta ɓaci a Zamfara kaɗai ba, ganin cewa sama da jihohi 20 na fama da irin wannan matsalar.
“Ina ganin idan za a ayyana dokar ta ɓaci a Zamfara, to ya kamata a yi hakan a wasu jihohi sama da 20.
Dangane da kiraye-kirayen amfani da dakarun haya daga ƙasashen waje domin yaƙi da ta’addanci, Jaji ya ce bai goyi bayan hakan ba.
Ya ce dakarun Nijeriya suna da ƙarfin da zai iya magance matsalar, muddin aka tallafa musu yadda ya kamata.
“Bai kamata mu nemi dakarun haya ba. Abin da muke buƙata shi ne a bai wa dakarunmu kayan aiki na zamani da kuma kulawa ta fuskar walwala. Idan aka ba su goyon baya da kayan aiki masu kyau, za su iya shawo kan ’yan ta’adda,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan bindiga Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda
Shirin zai kuma samar da dubban guraben aikin yi ga matasa, wanda hakan zai rage rashin aikin yi a ƙasar.
Mutanen karkara da manoma da suka fi fama da matsalolin tsaro za su fi amfana da wannan mataki.
Shugaba Tinubu ya jaddada cewa ba za a bar masu aikata laifuka suke cin karensu ba babbaka ba.
Ya ce gwamnati za ta wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a ko ina a cikin Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp