A ranar Talata ma, an sake kai hari a ƙauyen Kungurki.

Jaji, wanda ya taɓa zama Shugaban Kwamitin Tsaro da Leƙen Asiri a Majalisar Wakilai ta 8, ya ce bai dace a ayyana dokar ta ɓaci a Zamfara kaɗai ba, ganin cewa sama da jihohi 20 na fama da irin wannan matsalar.

“Ina ganin idan za a ayyana dokar ta ɓaci a Zamfara, to ya kamata a yi hakan a wasu jihohi sama da 20.

Matsalar tsaro ta zama ta ƙasa baki ɗaya, ba na yanki guda ba. Wannan ba siyasa ba ce. Idan ba mu ɗauki mataki yanzu ba, lamarin na iya shafar ƙasa gaba ɗaya,” in ji shi.

Dangane da kiraye-kirayen amfani da dakarun haya daga ƙasashen waje domin yaƙi da ta’addanci, Jaji ya ce bai goyi bayan hakan ba.

Ya ce dakarun Nijeriya suna da ƙarfin da zai iya magance matsalar, muddin aka tallafa musu yadda ya kamata.

“Bai kamata mu nemi dakarun haya ba. Abin da muke buƙata shi ne a bai wa dakarunmu kayan aiki na zamani da kuma kulawa ta fuskar walwala. Idan aka ba su goyon baya da kayan aiki masu kyau, za su iya shawo kan ’yan ta’adda,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan bindiga Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya tabbatar da cewa tattaunawar da suka yi da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ta kawo ƙarshen duk wata rigima da ke tsakaninsa da Gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara.

A daren ranar Alhamis ne Shugaba Tinubu, ya jagoranci wani zaman sulhu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, tsakanin Wike da Gwamna Fubara da kuma wasu daga cikin ’yan majalisar Ribas da aka dakatar.

NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe  Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji

Bayan ganawar, Wike ya yi magana da manema labarai, inda ya tabbatar da kawo ƙarshen rikicinsa da Fubara.

“Dukkaninmu mun amince mu yi aiki tare da Gwamna, kuma shi ma ya amince zai yi aiki da mu. Dukkanninmu ’yan gida ɗaya ne.

“Rigimarmu ta daɗe, amma zamanmu na ranar Alhamis ya kawo ƙarshenta. Dama ɗan Adam yana iya samun saɓani, amma daga baya a sasanta.”

Ya ƙara da cewa: “Kuma yau ne muka kammala komai, mun zo mun shaida wa Shugaban Ƙasa cewa mun daidaita. Don haka a gare ni, komai ya wuce.”

Wike, ya kuma yi kira ga mabiyansa da su kwantar da hankali tare da haɗa kai don ciyar da Ribas gaba.

“Ina kira ga kowa da kowa da mu haɗa kai da sauran jama’a. Babu sauran rigima, babu wani abu da za a sake yin faɗa a kai.”

Abin da rikicin ya haifar

A baya dai rikicin siyasa a Jihar Ribas, ya haifar da barazanar tsige Gwamna Fubara a watan Oktoban 2024, yayin daga bisani Shugaba Tinubu ya ayyana  dokar ta-ɓaci a watan Maris a jihar

Sai dai yanzu ɓangarorin sun ce komai ya wuce, kuma za su ci gaba da aiki tare domin ci gaban jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
  • Mutanen Sakkwato na neman ɗaukin gwamnati game da Bello Turji
  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
  • Har yanzu mun gaza gano dalilin ɓullar COVID-19 — WHO
  • Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau 
  • Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
  • Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja
  • Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike
  • Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
  • Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji