Aminiya:
2025-05-15@19:05:18 GMT

Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a Jigawa

Published: 15th, May 2025 GMT

Wutar lantarki ta kashe wani wanda ake zargin ɓarawon wayar rarraba wutar ne a harabar Sabuwar Sakatariyar Jihar Jigawa.

’Yan sanda sun sanar cewa an tsinci gawar mutumin ta maƙale ne a karkashin kankare da manyan wayoyin lantarkin ke ciki.

Kakakin ’yan sanda a Jihar Jigawa, Shiisu Lawal Adamu ya ce a safiyar ranar Alhamis ne suka samu kira daga Ma’aikatar Ayyuka ta Jihar Jigawa game da faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa tuni aka dauke gawar zuwa Babban Asibitin Dutse, domin gudanar da bincike.

 

 

 

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Horas Da Likitoci Akan Magance Tsananin Zazzabin Cizon Sauro

Gwamnatin jihar Kwara ta shirya wani gagarumin horo ga likitocin kiwon lafiya a fadin cibiyoyin kiwon lafiya na jihar kan yadda za a shawo kan cutar zazzabin cizon sauro.

 

Da yake sanar da bude horon a Ilorin, daraktan kula da lafiyar jama’a na jihar, Dokta Oluwatosin Fakayode, ya jadadda bukatar gaggawar gano cutar da wuri da kuma gaggauta magance cutar zazzabin cizon sauro, musamman a cikin mutane masu rauni kamar yara ‘yan kasa da shekaru biyar da mata masu juna biyu.

 

A cewarsa shirin ya kasance wani bangare na faffadan kokarin yaki da cutar zazzabin cizon sauro a jihar, gami da shirye-shiryen yakin rigakafin cutar zazzabin cizon sauro na 2025 (SMC).

 

Dokta Fakayode ya bayyana cewa horon zai kunshi zuwa gida-gida da maganin rigakafin zazzabin cizon sauro ga yara ‘yan watanni 3-59 a fadin kananan hukumomi 11 da suka cancanta a jihar Kwara.

 

Ya yi nuni da cewa har yanzu cutar zazzabin cizon sauro ta kasance babbar barazana ga lafiyar al’umma a Najeriya da jihar Kwara.

 

Dokta Fakayode ya yaba wa gwamnatin jihar bisa jajircewarta na kawar da cutar zazzabin cizon sauro da kuma saka hannun jarin da yake ci gaba da yi wajen karfafa karfin asibitoci a duk matakan kulawa.

 

A nata jawabin shugabar shirin na sashin zazzabin cizon sauro, Alhaja Latifat Abdullahi, ta bayyana jin dadin ta ga likitocin da suka halarci wannan taro kan sadaukarwar da suka yi a wannan fanni.

 

Ta jaddada mahimmancin ci gaba da haɓaka ƙwararru don samun ingantaccen sakamako na kiwon lafiya, ta ƙara da cewa ya kamata likitocin su yi amfani da sabbin dabarun da suka samu a aikace.

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kashi Na Biyu Na Maniyyata 415 Daga Jihar Kwara Sun Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
  • An Kaddamar da Shirin Karfafa Matasa Don Noman Kasuwanci A Kwara
  • NUJ Jigawa Ta Nada Wakilin Rediyon Tarayya A Matsayin Mamba Na Musamman
  • Gwamnati Kaduna Tace Zuba Jarin Da Ta Yi Na Euro Miliyan Dari Da Shadaya Zai Maganin Sufuri A Jihar
  • An Horas Da Likitoci Akan Magance Tsananin Zazzabin Cizon Sauro
  • Zabe Babu Hamayya: Isma’il Dutse Ya Karbi Ragamar NUJ Jigawa
  • Bom ya kashe jami’an ilimi 2 a Borno
  • Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar lantarki: ’Yan Najeriya sun yi tir da biyan diyya ga ’yan Band A