Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a Jigawa
Published: 15th, May 2025 GMT
Wutar lantarki ta kashe wani wanda ake zargin ɓarawon wayar rarraba wutar ne a harabar Sabuwar Sakatariyar Jihar Jigawa.
’Yan sanda sun sanar cewa an tsinci gawar mutumin ta maƙale ne a karkashin kankare da manyan wayoyin lantarkin ke ciki.
Kakakin ’yan sanda a Jihar Jigawa, Shiisu Lawal Adamu ya ce a safiyar ranar Alhamis ne suka samu kira daga Ma’aikatar Ayyuka ta Jihar Jigawa game da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa tuni aka dauke gawar zuwa Babban Asibitin Dutse, domin gudanar da bincike.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
Majalisar Dokokin Jihar Zamfara karkashin jagorancin Bashar Aliyu Gummi, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta hada kai da ayyukan tsaro a Jihar domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, kamar yadda babi na biyu na kundin tsarin mulki ya tanada.
A zaman taron na ranar Talata, mambobin sun yi zargin cewa, ‘yan bindiga sun mamaye al’ummomi da dama a fadin jihar Zamfara, kuma sun zargi Gwamnan da mayar da hankali kan burin siyasa da kuma zargin abokan hamayya.
Sun kuma yi zargin cewa, Gwamnan bai kai ziyara ko aika tallafi ga al’ummomin da hare-hare ya shafa ba, inda suka ce ziyarar da ya shirya kai wa al’ummar Banga da ke karamar hukumar Kaura Namoda ta kasance da alaka da siyasa gabanin zaben fidda gwani na majalisar dokokin jihar.
A nasa gudunmuwar, Bashir Abubakar Masama na Bukkuyum ta Arewa ya yabawa kokarin gwamnatin tarayya na yaki da ‘yan fashi, inda ya bayyana cewa Adapka, Zauma, Gwashi, da Mayanchi a mazabarsa sun sha fama da hare-hare akai-akai.
Da yake goyon bayan kudirin, Bashir Bello Sarkin Zango na Bungudu ta Yamma, ya yi zargin cewa, Gidan Bugaje, Zaman Gida, Kukan Tara, da Gidan Dan-Inna, gungun miyagu sun mayar da yankin nasu, yayin da shugaban marasa rinjaye Aliyu Ango Kagara na Talata Mafara ta Kudu ya sanya Morai, Bobbo, Makera, Jangebe, Gwaram, da Ruwan Gizo a matsayin kauyukan da lamarin ya fi shafa a mazabarsa.
‘Yan majalisar sun bukaci gwamnatin tarayya da ta yi watsi da gwamnatin jihar a harkokin tsaro.
Sun yi kira ga mazauna yankin da su kasance masu bin doka da oda tare da bayar da sahihan bayanai ga hukumomin tsaro.
A nasa bangaren, Ibrahim Tudu Tukur na Bakura ya yi zargin cewa al’ummarsa na ci gaba da zama a killace da ‘yan bindiga, inda ya bayar da misali da harin da aka kai a kwanan nan a Damri, Dakko, Sama, Sabon Garin Damri, da Sade, yayin da Faruk Musa Dosara na Maradun ya yi kira da a duba yiwuwar tsige Gwamnan bisa zarginsa da yin sakaci da aikinsa.
Ya kuma jaddada bukatar mazauna yankin su baiwa jami’an tsaro sahihin bayanai kan duk wani nau’in da ake zargi da aikata laifuka domin a kama su kafin su aikata wani laifi.
Sun kuma yi alkawarin ci gaba da yin kira da a samar da shugabanci na gari a Zamfara domin ci gaban jihar.
AMINU DALHATU.