Wasu yan jaridu masu bincike a kasar Amurka sun gano sunan sojan HKI wanda ya bindige yar rahoton tashar Aljazeera ta kasar Qatar a shekara ta 2022 a lokacinda take Shirin bada rahoton hare-harenn da sojojin yahudawan suke kaiwa kan wata unguwa ta Falasdinawa a birnin Jenin na yankin yamma da Kogin Jordan.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wadanda suka shirya film na tattara bayanai yadda aka kashe Shirin Abu Akela wato ‘ Zeteo’ dake da cibiya a birnin Washington na kasar Amurka na cewa sunan sojan HKI ta ya kashe Shirin shi ne Alon Skajio, wanda shima daga baya an kashe shi a birnin na Jenin daga bayan a wani farmakin da sojojin yahudawan suka kai cinin birnin.

Majigin mai tsaron mintuna 40 ya bayyana yadda gwamnatin Amurka ta shugaba Biden ta yi kokarin boye sunan wanda ya kashe yar jaridar da kuma wanke HKI kan wannan laifin da ta aikata na kashe yan jaridu.

Alon ya kashe Shirin yar shekara 51 a duniya da bindiga wanda ake cillawa daga nesa wato Sniper al-hali a fili yake tana sanye da kayakin yan jaridu wadanda aka rubuta Press a kansa a ranar 26 ga watan Mayun shekara ta 2022. Banda haka sojojin sun kai farmaki kan gawarta a lokacin jana’izata.

An haifi Abu Akleh a birnin al-Quds a shekara 1971 sannan tana da dijiri kan aikin jarida daga jami’ar Yarmouk ta kasar Jordan sannan ta fara aikin da tashar talabijin ta Al Jazeera a shekara ta 1977.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina

Ƙaramar Hukumar Sabuwa da ta Ɗandume a Jihar Katsina sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, a wani yunƙuri na kawo ƙarshen hare-hare, kashe-kashe da sace-sacen da suka daɗe suna addabar yankin.

An gudanar da taron sulhun ne a ranar Asabar a ƙauyen Kabalawa Dungun Mua’zu, da ke iyaka da ƙananan hukumomin biyu, amma yana ƙarƙashin Sabuwa.

Da wannan ci-gaban, adadin ƙananan hukumomi da suka ƙulla yarjejeniyar sulhu da ’yan bindiga a jihar ya kai tara.

Sauran sun haɗa da Batsari da Kankara, Kurfi da Musawa da Ɗanmusa da Jibia da kuma Faskari.

Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu

Shugaban Ƙaramar Hukumar Sabuwa, Sagir Tanimi, da takwaroransa na Ɗandume, Bashir Gyazama, sun halarci taron, inda aka ce su ne suka taimaka wajen cimma yarjejeniyar.

Taron wanda ya ɗauki sa’o’i da dama ya haifar da wasu muhimman matsaya da ɓangarorin biyu suka cimma.

An amince da dakatar da kai hari, inda ’yan bindiga suka yi alƙawarin daina kai hare-hare a ƙauyuka.

Haka kuma an ba su damar shiga garuruwa da ƙauyuka domin harkokin kasuwanci ba tare da tsoron cutarwa daga jama’a ba.

Bugu da ƙari, ’yan bindigar sun yi alƙawarin sako mutanen da suka yi garkuwa da su, sai dai sun roƙi gwamnati ta yi ƙoƙarin ganin an saki ’ya’yansu da ke tsare.

Ɓangarorin biyu sun kuma sha alwashin yin aiki tare domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

A yayin taron, ’yan bindiga da dama sun halarta ɗauke da manyan makamai, tare da shugabanninsu da suka haɗa da Idi Muwage da Alhaji Kabiru da Kachalla Rusku da Kachalla Murtala da Kachalla Mai Saje da Kachalla Dawa da Ardo Abdulsalam Fatika da kuma Alhaji Labi.

Shugaban kwamitin zaman lafiya, Dakta Salisu Ladan, ya bayyana cewa manufar yarjejeniyar ita ce dawo da zaman lafiya mai ɗorewa da kawo ƙarshen kashe-kashe da garkuwa da mutane da sauran munanan ayyuka.

Ya ƙara da cewa, “Shugabannin yankin sun tabbatar wa ’yan bindigar da tsaron rayukansu tare da maraba da su don su ci gaba da gudanar da harkokin kasuwanci a kasuwannin yankin.”

Haka kuma an cimma matsaya cewa za a buɗe kasuwar shanu ta Ɗandume da aka rufe saboda matsalar tsaro, domin bai wa ’yan bindigar damar kawo dabbobinsu da yin ciniki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Kama Masu Laifi
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
  • Mahara sun kashe ɗan sanda, sun ɗauke bindigarsa a Taraba
  • ‘Yan Gwagwarmaya  Sun Kashe Sojojin Mamaya Biyu A Wani Kwanton Bauna A Arewacin Gaza
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Yawan Kudin Da Aka Kashe Na Zamantakewa A Watan Agusta A Kasar Sin Ya Kai RMB Triliyan 3.97
  • Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya
  • Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Gilla Kan Fararen Hula 5 A Kudancin Kasar Lebanon
  • An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike