Aminiya:
2025-11-08@18:06:07 GMT

An kama mutum 6 da ake zargi kan garkuwa da mutane

Published: 8th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Akwa Ibom ta ce, ta kama wasu mutum shida da ake zargi da yin garkuwa da wasu mutane a jihar kwanan nan.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, DSP Timfon John ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya sanarwa manema labarai a ranar Alhamis a garin Uyo, inda ya ce an kama su ne biyo bayan sahihan bayanai game da shirin yin garkuwa da mutane a ƙaramar hukumar Eket.

A yi amfani da fasahar zamani don yaƙar ta’addanci — Ganduje Sojoji sun kama mutum 4 kan zargin ta’addanci a Taraba

John wanda ya bayyana cewa mace ɗaya tilo a cikin waɗanda ake zargin ba ’yar Najeriya ba ce, ya bayyana cewa an ƙwato wata mota ƙirar leɗus da wayoyin hannu guda biyar daga hannun waɗanda ake zargin.

“A bisa wannan bayanin, jami’an rundunar sun tattara kadarori, inda suka kama wani mutum mai suna Joseph Alafia, a Garin Oron a ranar 6 ga Mayu, 2025. Wannan kamun na farko ya ƙara kai samame wurare biyu a Afia Nsit Eket.

“Waɗannan ayyuka da rundunar ’yan sandan ta gudanar tare da haɗin guiwa sun yi nasarar cafke wasu mutane kamar haka: Oyibo Ayibakumo Brown, namiji ɗan Jihar Bayelsa, Wisdom Harry, namiji ɗan Jihar Ribas, Afanye Igonikon, namiji dan Jihar Ribas, Dare Olaniyi, namiji ɗan Jihar Ogun, da ke zaune a garin Port Harcourt,  Jihar Rivers da kuma Tita Mercy Masume mace ’yar ƙasar Kamaru.

“A yayin samamen, hukumomi sun gano motar Lexus RX 300 mai lamba KMR 491 AE mai launin toka, waɗanda ake zargin ana amfani da su wajen yin garkuwa da mutane, tare da wayoyin hannu guda biyar.

“Waɗanda aka kama ana kyautata zaton suna da alaƙa da sace-sacen da aka yi a Eket na baya-bayan nan, kuma a halin yanzu ana gudanar da bincike mai zurfi.

“Kwamishanan ’Yan sanda, CP Baba Mohammed Azare fsi, ya yaba da yadda jami’an ’yan sandan suka yi taka-tsan-tsan da ɗaukar matakin da suka ɗauka na samun nasarar kamen.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Akwa Ibom Masu Garkuwa da mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas Ta Goyi Bayan Matakin shari’ar Turkiyya Kan Neman kama Masu Take Hakkin Bil’Adama A Isra’ila

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta yi tsokaci kan yadda bangaren shari’a na Turkiyya ya bayar da sammacin kama Netanyahu fira ministan Isra’ila

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta yaba da fitar da sammacin neman kama jami’an haramtacciyar kasar Isra’ila 37, ciki har da shugaban gwamnatin mamayar, Netanyahu mai aikata laifukan yaki, da ministocin tsaro Gallant da Katz.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a daren Juma’a, kungiyar ta ce wannan matakin “ya tabbatar da matsayin al’ummar Turkiyya da shugabancinsu, wadanda suka jajirce kan kyawawan dabi’un adalci da dan Adam, da kuma ‘yan uwantaka da ke tsakaninsu da al’ummar Falasdinawa da ake zalunta.”

Kungiyar Hamas ta jaddada cewa: “Al’ummar Falasdinawa na ci gaba da fuskantar mummunan yakin kawar da mutane a tarihin zamani a hannun masu aikata laifukan yaki tsakanin shugabannin mulkin kama-karya,” kamar yadda ta bayyana su.

Hamas ta kuma yi kira ga dukkan kasashen duniya da hukumomin shari’arsu da su bi sahun kasar Turkiyya wajen bayar da sammacin kama mutane masu aikata muggan laifuka da kuma bin diddigin shugabannin mamayar Sahayoniyya a ko’ina, da kuma yin aiki don kawo su gaban shari’ar kasa da kasa da kuma hukunta su kan laifukan da suka aikata kan bil’adama.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tarayyar Afirka Ta Yi Kiran Da A Girmama ‘Yancin Kai Na Najeriya Da Rashin Tsoma Baki A Harkokin Gidanta November 8, 2025  Tanzania: An Tuhumi Mutane Da Dama Da Laifin Cin Amanar Kasa Bayan Rikicin Zabe November 7, 2025 Limamin Juma’ar Tehran: Tsayin Dakan ‘Yan Gwagwarmaya Daga Koyi Ne Da Alkur’ani Mai Girma November 7, 2025 Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan November 7, 2025 Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan November 7, 2025 Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon November 7, 2025 Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza November 7, 2025 Falasdinawa Miliyan 1.5 Ne Ke Cikin Mawuyacin Hali November 7, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya November 7, 2025 An Rantsar Da Paul Biya A Matsayin Shugaban Kamaru Karo Na Takwas November 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Barau Zai Yi Ƙarar Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
  •  Lebanon: Mutane 2 Sun Jikkata Sanadiyyar Harin “Isra’ila” A Garin Bint-Jubail
  • Hamas Ta Goyi Bayan Matakin shari’ar Turkiyya Kan Neman kama Masu Take Hakkin Bil’Adama A Isra’ila
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  •  Tanzania: An Tuhumi Mutane Da Dama Da Laifin Cin Amanar Kasa Bayan Rikicin Zabe
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu