Aminiya:
2025-06-23@06:23:14 GMT

An kama mutum 6 da ake zargi kan garkuwa da mutane

Published: 8th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Akwa Ibom ta ce, ta kama wasu mutum shida da ake zargi da yin garkuwa da wasu mutane a jihar kwanan nan.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, DSP Timfon John ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya sanarwa manema labarai a ranar Alhamis a garin Uyo, inda ya ce an kama su ne biyo bayan sahihan bayanai game da shirin yin garkuwa da mutane a ƙaramar hukumar Eket.

A yi amfani da fasahar zamani don yaƙar ta’addanci — Ganduje Sojoji sun kama mutum 4 kan zargin ta’addanci a Taraba

John wanda ya bayyana cewa mace ɗaya tilo a cikin waɗanda ake zargin ba ’yar Najeriya ba ce, ya bayyana cewa an ƙwato wata mota ƙirar leɗus da wayoyin hannu guda biyar daga hannun waɗanda ake zargin.

“A bisa wannan bayanin, jami’an rundunar sun tattara kadarori, inda suka kama wani mutum mai suna Joseph Alafia, a Garin Oron a ranar 6 ga Mayu, 2025. Wannan kamun na farko ya ƙara kai samame wurare biyu a Afia Nsit Eket.

“Waɗannan ayyuka da rundunar ’yan sandan ta gudanar tare da haɗin guiwa sun yi nasarar cafke wasu mutane kamar haka: Oyibo Ayibakumo Brown, namiji ɗan Jihar Bayelsa, Wisdom Harry, namiji ɗan Jihar Ribas, Afanye Igonikon, namiji dan Jihar Ribas, Dare Olaniyi, namiji ɗan Jihar Ogun, da ke zaune a garin Port Harcourt,  Jihar Rivers da kuma Tita Mercy Masume mace ’yar ƙasar Kamaru.

“A yayin samamen, hukumomi sun gano motar Lexus RX 300 mai lamba KMR 491 AE mai launin toka, waɗanda ake zargin ana amfani da su wajen yin garkuwa da mutane, tare da wayoyin hannu guda biyar.

“Waɗanda aka kama ana kyautata zaton suna da alaƙa da sace-sacen da aka yi a Eket na baya-bayan nan, kuma a halin yanzu ana gudanar da bincike mai zurfi.

“Kwamishanan ’Yan sanda, CP Baba Mohammed Azare fsi, ya yaba da yadda jami’an ’yan sandan suka yi taka-tsan-tsan da ɗaukar matakin da suka ɗauka na samun nasarar kamen.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Akwa Ibom Masu Garkuwa da mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos

Mahara sun sake kai hari tare da kashe akalla mutum 17 a kananan hukumomin Mangu da Bokkos na jihar Filato.

Rahotanni sun nuna an kai harin ne ranar Alhamis a kauyen Manja da ke masarautar Chakfem a Mangu da kuma kauyen Tangur da ke Bokkos.

Bayanai sun nuna maharan sun farmaki yankunan ne a lokuta daban-daban.

2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’ Za mu iya galaba kan Iran ko babu Amurka — Isra’ila

Yayin da aka kai harin Tangur wajen misalin karfe 9:00 na dare, shi kuma na Manja an kai shi ne tun da gefen almuru.

Majiyoyi daga yankunan sun ce maharan sun bude wuta suka karkashe mutanen kafin daga bisani su cika wandunansu da iska.

A cewar majiyoyin, an kashe mutum bakwai a Mangu, a Bokkos kuma mutum 10.

Sun kuma ce maharan, wadanda ke dauke da bindiga sun rika harbin kan mai uwa da wabi sannan suka rika haura gidajen mutane suna karkashe su.

Daraktan Al’adu na kungiyar Ci Gaban Mwaghavul, Shohotden Mathias Ibrahim, da kuma Daraktan da ke kula da sansanin ’yan gudun hijira na Mangu ne suka tabbatar da alkaluman mutuwar, inda suka ce yanzu haka ana zaman dardar a yankin.

Sai dai ya zuwa yanzu, shugabannin al’umma da kuma mazauna yankin ba su amsa sakon da wakiliyarmu ta tura musu na neman karinn bayani ba.

Kazalika, rundunar ’yan sandan jihar Filato ba ta magantu a kan hare-haren ba, sakamakon Kakakin runduna, Alfred Alabo, bai amsa kiran waya da sakon kar-ta-kwana da na Whatsapp din da wakiliyarmu ta tura masa ba, ya zuwa lokacin hada wannan rahoton.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani
  • Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno
  • Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5
  • Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda
  • Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
  • Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna
  • Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
  • Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
  • Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo
  • Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos