Har ila yau, kwamitin zai bada shawara akan hukuncin da Jam’iyar za ta dauka Idan har aka sami wanda ake zargi da laifin almundahana da kuma zagon Kasa ga LP a lokacin da yake Shugabantar jam’iyar.

 

Sanata Usman ta zargi Abure da mukarrabansa da aikata laifufuka dake janyo rabuwar Kai ga ‘ya’yan Jamiyar tare da batanci da haddasa rikici.

 

Sanata Usman ta Kara da cewa, Abure yana aikata laifufuka wanda suke kalubalantar mutunci Jam’iyar da kuma yin karo da manufofin dimokuradiyya. Don haka, majalisar zartaswa ta Jam’iyar ta dauki matakin kaddamar da bincike kan wannan munanan halayya.

 

Bugu da Kari Sanata Nenadi Usman tace majalisar zantaswa na Jamiyar Labour bayan dogon nazari akan hukuncin da kotun koli ta Kasa ta yi na ranar 4 ga watan Afrilun 2025, Jam’iyar ta nuna matukar damuwarta akan Yadda Julius Abure yake amfani da sunan shi a matsayin Shugaban Jam’iyar bayan wa’adin jagorancin shi ya cika.

 

Ta ce, abubuwan da Julius Abure yake yi ya sabawa dokar Kasa kuma ya ci mutuncin Jamiyar. A sabo da haka ne tace kundin tsarin mulkin Jamiyar na shekarar  2019 (Wanda aka yi wa Kwaskwarima) ya Basu damar daukan kwararan matakai da hukunci akan Julius Abure.

Daga bisani, Sanata Nenadi Usman ta nuna rashin amincewarta akan Yadda Julius Abure yake cin mutunci jagoran jam’iyar Labour na Kasa, Peter Obi da Gwamna Alex Otti. Tace Abure da mukarabansa wadanda wa’adinsu ya kare, basu da hurumin magana da yawun Jam’iyar kuma baza su iya dakatar da Gwamnan ba ko wani mamban Jamiyar.

 

Ta kuma shaidawa ‘Yan Nijeriya cewa, Jam’iyar ta sanar da Hukumar Zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) akan shirye-shiryenta na gudanar da zabuka a matakai daban-daban tare da gudanar da babban taron Jam’iyar na kasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

Aƙalla mutum 10 ne suka rasu a daren ranar Juma’a bayan wani ɗan ƙunar baƙin wake ya kai hari da bam a wani wsjen cin abinci da ke garin Konduga, a Jihar Borno.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Borno, ASP Nahum Daso, ya tabbatar da faruwar lamarin.

’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano

Ya ce jami’an tsaro da suka haɗa da ‘yan sanda da sojoji na gudanar da bincike domin gano haƙiƙanin abin da ya faru da kuma adadin waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Ya ce, “Wani mutum ya kutsa cikin taron mutane da misalin ƙarfe 10 na dare tare da bam, wanda ya tarwatsa kansa kuma ya kashe sama da mutum 10.”

Wani masani kan ta’addanci, Zagazola Makama, ya bayyana cewa mutum 24 ne, suka rasu a sanadin harin, inda ya ce mace ce ta kai harin ƙunar baƙin waken.

Ya ƙara da cewa fashewar ta yi tsanani wanda sai kan matar aka samu.

Bayan harin, an tura tawagar sojoji, ƙwararrun masu binciken bam na ‘yan sanda, ’yan sa-kai, da ƙungiyar CJTF zuwa wajen.

Sun yi bincike amma ba su samu bam na biyu a wajen ba.

An kwashe waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH) domin a kula da su.

An kai gawarwakin waɗanda suka rasu zuwa asibitin kuma likitoci sun tabbatar da rasuwarsu.

Makama, ya ce ana ci gaba da tantance sunayen waɗanda abin ya rutsa da su domin a miƙa gawarwakinsu ga iyalansu domin yi musu jana’iza.

Kai harin ƙunar baƙin wake na ɗaya daga cikin dabarun da ƙungiyar Boko Haram ta fara amfani da su a farko-farkon fara ta’addancinta a Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2
  • Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran
  • Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS
  • Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
  • Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato
  • Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno
  • Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila
  • Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila
  • Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi daraja a Isra’ila