’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato
Published: 8th, May 2025 GMT
’Yan sanda sun gano harsasai guda 500 a wata maɓoyar masu aikata laifuka da ke kusa da hanyar Bauchi a Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Emmanuel Adesina, ya ce an gano harsasan ne ta hanyar rahotannin sirri, inda ya bayyana hakan a matsayin babbar nasara a yaƙi da aikata laifuka a jihar.
Kwamishinan ya ci gaba da bayanin cewa an gano harsasan ne bayan wani kisan kai da ya faru a yankin, inda aka kashe wani da ba a gane ko wanene ba.
“Bayan samun rahoton faruwar lamarin, nan take muka fara gudanar da bincike domin gano yanayin da ya kai ga mutuwar wanda aka kashe.
An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’ ’Yan sanda sun bankaɗo masana’antar man gyaɗa na bogi a Kaduna“A yayin gudanar da wannan binciken ne aka samu nasarar gano waɗannan harsasan. Ina so in ba ku tabbacin cewa muna ci gaba da ƙoƙarin ganowa tare da kama waɗanda suka aikata wannan laifin tare da ƙwato makamansu.”
Ya yi kira ga al’ummar jihar da su ba su duk wani bayani da zai iya taimakawa wajen kama su.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun IRGC: Iran Za Ta Tarwatsa Makiya Tare Da Mayar Da Martani Kan Duk Wani Zalunci
Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci na Iran sun bayyana cewa: Duk wani sabon kuskuren lissafin makiya zai fuskanci mayar da martani mai muni
A cikin wata sanarwa da suka fitar a farkon makon tsaro mai alfarma, na ranar tunawa da arangama da gwamnatin Saddam ta yi da Jamhuriyar Musulunci ta Iran a tsakanin shekarun 1980-1988, dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran (IRGC) sun jaddada cewa: Duk wani sabon kuskuren lissafi da makiya za su yi, za su fuskanci mummunan martani da zai zame babban darasi a gare su.
A cikin bayanin da suka yi na farkon makon tsaro na dakarun IRGC sun bayyana cewa: A hakikanin gaskiya makon tsaro, biki ne na nasarar gwagwarmayar jama’a, kuma abin tunawa na daya daga cikin manyan abubuwa mafiya haske a tarihin juyin juya halin Musulunci, sannan abin alfahari ga kasar, kuma abin alfahari ne a duniya. Sannan tsaro mai alfarma wani zamani ne da al’ummar Iran bisa dogaro da imani da hadin kai da jagorancin Ubangiji suka samu nasarar dakile duk wani yunkuri na gaba daya da makiya da suka shirya a kan iyakokin kasar Iran da juyin juya halin Musulunci da tsarin Musulunci da kuma kiyaye martaba da ‘yancin kai da cikakken yankin kasar daga makircin masu girman kai.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen: ‘Yan Koren Amurka Da Isra’ila Suke Neman Wargaza Hadin Kan Larabawa Da Na Musulmi September 22, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Gilla Kan Fararen Hula 5 A Kudancin Kasar Lebanon September 22, 2025 Ministan Harkokin Waken Falasdinu Ta Yi Kira Ga Karin Kasashe Su Amince Da Samuwar Kasarta September 21, 2025 Iran Da Pakistan Sun Sake Tsara Dangantakarsu Ta Tattalin Arziki September 21, 2025 Trump Ya Bukaci Afganistan Ta Mayarwa Amurka Sansanin Jiragen Sama Na bagram September 21, 2025 Kasashen Ingila Da Canada Da Kuma Australia Sun Bayyana Amincewarsu Da Samuwar Kasar Falasdinu September 21, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kira Ga Samar Da Tattalin Arziki Da Shugabancin Kwararru September 21, 2025 Arakci Ya Kore Cewa Ya Zanta Da Steven Witkoff Na Amurka September 21, 2025 Hizbullah Ta Yi Gayyar Tunawa Da Zagayowar Shahadar Sayyid Hassan Nasrallah September 21, 2025 Hamas Ta Yi Bukaci A Hukunta HKI Akan Rusa Asibitoci September 21, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci