’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato
Published: 8th, May 2025 GMT
’Yan sanda sun gano harsasai guda 500 a wata maɓoyar masu aikata laifuka da ke kusa da hanyar Bauchi a Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Emmanuel Adesina, ya ce an gano harsasan ne ta hanyar rahotannin sirri, inda ya bayyana hakan a matsayin babbar nasara a yaƙi da aikata laifuka a jihar.
Kwamishinan ya ci gaba da bayanin cewa an gano harsasan ne bayan wani kisan kai da ya faru a yankin, inda aka kashe wani da ba a gane ko wanene ba.
“Bayan samun rahoton faruwar lamarin, nan take muka fara gudanar da bincike domin gano yanayin da ya kai ga mutuwar wanda aka kashe.
An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’ ’Yan sanda sun bankaɗo masana’antar man gyaɗa na bogi a Kaduna“A yayin gudanar da wannan binciken ne aka samu nasarar gano waɗannan harsasan. Ina so in ba ku tabbacin cewa muna ci gaba da ƙoƙarin ganowa tare da kama waɗanda suka aikata wannan laifin tare da ƙwato makamansu.”
Ya yi kira ga al’ummar jihar da su ba su duk wani bayani da zai iya taimakawa wajen kama su.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya nuna baƙin cikinsa kan kisan wasu matafiya daga Jihar Kaduna da aka yi a Ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.
Matafiyan sun fito ne daga Zariya suna kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure, yayin da wasu ɓata-gari suka farmake su.
HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba SaniGwamnan ya ce wannan kisa abin takaici ne kuma rashin imani ne da ya saɓa wa doka.
Ya buƙaci a yi adalci cikin gaggawa.
Haka kuma ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kaduna, iyalan mamatan, da sauran waɗanda abin ya shafa.
A cewar sanarwar da Daraktan Yaɗa Labaran Gwamnatin Jihar Gombe, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar, Gwamna Yahaya ya yaba wa gwamnati da ‘yan sanda a Jihar Filato bisa kamo wasu da ake zargi da hannu a kisan.
Gwamnan ya buƙaci a yi bincike na gaskiya, a gurfanar da waɗanda ke da hannu domin a hukunta su, sannan a hana irin hakan faruwa a gaba.
Haka kuma, ya roƙi al’ummar Filato da Kaduna da sauran maƙwabta da su zauna lafiya, su guji ɗaukar fansa.
Ya ce Gwamnonin Arewa za su ci gaba da haɗa kai domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin.
“Ina tabbatar muku cewa kare rayuka da dukiyoyin al’umma shi ne babban burinmu. Za mu yi aiki tare har sai an kawo ƙarshen wannan matsala,” in ji Gwamnan.