’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato
Published: 8th, May 2025 GMT
’Yan sanda sun gano harsasai guda 500 a wata maɓoyar masu aikata laifuka da ke kusa da hanyar Bauchi a Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Emmanuel Adesina, ya ce an gano harsasan ne ta hanyar rahotannin sirri, inda ya bayyana hakan a matsayin babbar nasara a yaƙi da aikata laifuka a jihar.
Kwamishinan ya ci gaba da bayanin cewa an gano harsasan ne bayan wani kisan kai da ya faru a yankin, inda aka kashe wani da ba a gane ko wanene ba.
“Bayan samun rahoton faruwar lamarin, nan take muka fara gudanar da bincike domin gano yanayin da ya kai ga mutuwar wanda aka kashe.
An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’ ’Yan sanda sun bankaɗo masana’antar man gyaɗa na bogi a Kaduna“A yayin gudanar da wannan binciken ne aka samu nasarar gano waɗannan harsasan. Ina so in ba ku tabbacin cewa muna ci gaba da ƙoƙarin ganowa tare da kama waɗanda suka aikata wannan laifin tare da ƙwato makamansu.”
Ya yi kira ga al’ummar jihar da su ba su duk wani bayani da zai iya taimakawa wajen kama su.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sharhin bayan Labarai: Ci Gaban Harkokin Kasuwanci Tsakanin Iran Da Kasashen Waje Duk Tare Da Takunkuman Kasashen Yamma
Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da “Bankasar tattalin arzikin Iran duk tare da takunkuman tattalin arziki masu tsanani wadanda kasashen yamma musamman Amurka suka doramata, wanda ni tahir amin zan karanta.
////…A dai-dai lokacinda gwamnatin kasar Amurka take barazanar zata hana sayan danyen man fetur daga kasar Iran kwatakwata, sannan take barazanar zata farwa kasar da yaki saboda shirin na makamashin nukliya, sabbin rahotanni sun bayyana cewa iran tana gaba a fitar da kayaki kasuwanci zuwa kasar China sannan ita ce ta 9 a duniya wajen samar da kwan kaji da sauran tsuntsaye.
Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya bayyana cewa, yawan danyen man fetur wanda kasar Iran take sayarwa kasar China kadai ya kai ganga miliyon 1.8 a ko wace rana a cikin watan Mayun da ya gabata na wannan shekara ta 2025.
Labarin ya kara da cewa kasar Iran a halin yanzu tana sayarwa kasashe 110 kayakin abinci na halal, wadanda suka hana da nama da sauran kayakin abincin na dabbobi. Kuma ita ce kasa ta 9 a duniya wajen samar da kwan suntsaye.
A wani labarin kuma yankin ciniki mara shinge na Aras ya samar da kudaden shiga ga kasar wanda ya kai dalar Amurka miliyon $200 a shekara ta 2024 da ta gabata. Hadi Moghaddamzadeh, shugaban yankin ya bayyana cewa yankin nasa ya samar da kudaden shiga hard alar Amurka miliyon 200, a arewa maso yammacin kasar kuma kudaden shigan da aka samu daga kasar Azerbaijan kadai ya kai dalar Amurka miliyon 11.
A lokacinda yake magana da kamfanin dillancin labaran Pars today a gefen kasuwar baje koli na Iran Expo 2025 wanda aka gudanar a nan Tehran Moghaddamzadeh ya kara da cewa yankin ciniki mara shingen na Aras ya fi muhimmanci a kan sauran iran wannan yankunan da ake da su a nan kasar Iran, saboda wuraren yawon bude ido da shakatawa da yankin yake da su.
A bangaren sayar da kayakin abinci wanda ake kira Halal kuma, shi ne kayakin da iran take fitarwa zuwa kashe kimani 110 a duniya, kuma yake gaza da wasu kasashe a wannan bangaren.
Darakta mai kula da wannan bangaren, ya ce kayakin abinci na Halal wadanda suke fita daga kasar Iran suna zuwa kasashen kamar Malaysia, Singapore, kasashen yankin tekun farisa, arewacin Africa da sauransu.
Ya ce a yankin dai kayakin abinci daga Iran suna shiga kasashen Iraq, Turkiyya, UAE, Afghanistan, Russia, da wasu kasashen Turai.
Sannan shugaban kwastom na Jolfa, ya bayyana cewa a watan da ya gabata, kayakin abince na kimani dalar Amurka miliyon 8.5 suka fita da kofar fitar da kayaki kasuwanci a yankinsa a watan da ya gabata kadai.