An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’
Published: 8th, May 2025 GMT
An kwantar da wasu matan aure kishiyoyin juna a asibiti bayan da suka sha maganin kara sha’awa domin burge mijinsu bayan ya auro mata ta uku.
Kishiyoyin biyu da ke yankin Dakwa a Abuja sun sha maganin gargajiyan, wanda aka fi sani da kayan mata ne, kwana uku bayan amaryar da mijinsu ya auro ta tare.
Da take tabbatar da faruwar lamarin, mijin nasu ya ce bayan kai su asibiti ne aka yi musu gwaji aka gano cewa wasu gaɓoɓinsu sun samu matsala, wanda ake zargin maganin da suka sha ne ya haddasa.
Ya ce, “ina gidan amarya aka kira ni cewa matana ba su da lafiya, inda na je na samu suna birgima cewa cikinsu na ciwo. Sai na kira wata nas ta duba su ta su magani ta yi musu ƙarin ruwa amma basu sani ba.
“Shi ne sai da muka kai su asibitin Madallah da ke Jihar Neja.
“A nan ne aka yi musu gwaji aka gano cewa wasu gaɓoɓinsu sun samu matsala, aka yi musu aiki,” in ji shi.
Magidancin mai suna Musa Muhammad ya bayyana cewa sallamo matan nasa a ranar Litinin, kuma an gano cewa sun sayi kayan matan ne a wajen wata wata mai tallar maganin gargajiya da suka saba saya.
Magidancin wanda ya ce yana ƙoƙarin gano matar domin kare wasu mata daga faɗawa a tarkonta, ya bayyana cewa matan nasa sun saba maganin na ruwa a wurin matar wanda suke haɗawa da madara, amma a wannan karon sai ta canza ta ba su na gari.
Shan kayan mata na daga cikin abubuwan da suka zama ruwan dare a tsakanin mata, inda masana kiwon lafiya ke gargaɗi game da haɗarinsi ga lafiyarsu da matucinsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Amarya Kayan Mata Maganin Gargajiya
এছাড়াও পড়ুন:
An sace jaririya sa’o’i kaɗan bayan haihuwarta a asibitin Ekiti
An nemi wata jaririya sa’o’i kaɗan bayan haihuwarta an rasa a Cibiyar Lafiya ta Okeyinmi da ke Ado-Ekiti, babban birnin Jihar Ekiti, a ranar Litinin.
Wani ganau ya ce an gano ɓatan jaririyar ne lokacin da ma’aikatan jinyar da ke bakin aiki suka je su duba lafiyarta da safiyar wannan Litinin ɗin.
Za a samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya na kwanaki uku a faɗin Nijeriya — NiMet Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙuraLamarin na ba-zato-ba-tsammani ya haifar da fargaba musamman yadda ɗimauta uwar jaririyar da kuma wasu daga cikin mutanen da ke cikin harabar asibitin.
Tuni dai an garzaya da ma’aikatan da ke kula da ɗakin haihuwa da uwar jaririyar da mai gadi da wasu da ake zargi zuwa ofishin ’yan sanda domin ci gaba da bincike.
Aminiya ta ruwaito cewa wasu masu neman na abinci a kusa da asibitin sun shiga ɗimuwa matuƙa dangane da faruwar lamarin.
Mai magana da yawun rundunar ’yan sanda na jihar, SP Sunday Abutu, ya ce yanzu haka akwai mutum huɗu da ake zargi da suka shiga hannu, “kuma suna bayar da bayanai masu amfani da za su taimaka a binciken.”
Abutu ya ce Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Mista Joseph Eribo, ya umurci sashen bincike na musamman (CID) da su gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da dawo da jaririyar cikin ƙoshin lafiya.