An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’
Published: 8th, May 2025 GMT
An kwantar da wasu matan aure kishiyoyin juna a asibiti bayan da suka sha maganin kara sha’awa domin burge mijinsu bayan ya auro mata ta uku.
Kishiyoyin biyu da ke yankin Dakwa a Abuja sun sha maganin gargajiyan, wanda aka fi sani da kayan mata ne, kwana uku bayan amaryar da mijinsu ya auro ta tare.
Da take tabbatar da faruwar lamarin, mijin nasu ya ce bayan kai su asibiti ne aka yi musu gwaji aka gano cewa wasu gaɓoɓinsu sun samu matsala, wanda ake zargin maganin da suka sha ne ya haddasa.
Ya ce, “ina gidan amarya aka kira ni cewa matana ba su da lafiya, inda na je na samu suna birgima cewa cikinsu na ciwo. Sai na kira wata nas ta duba su ta su magani ta yi musu ƙarin ruwa amma basu sani ba.
“Shi ne sai da muka kai su asibitin Madallah da ke Jihar Neja.
“A nan ne aka yi musu gwaji aka gano cewa wasu gaɓoɓinsu sun samu matsala, aka yi musu aiki,” in ji shi.
Magidancin mai suna Musa Muhammad ya bayyana cewa sallamo matan nasa a ranar Litinin, kuma an gano cewa sun sayi kayan matan ne a wajen wata wata mai tallar maganin gargajiya da suka saba saya.
Magidancin wanda ya ce yana ƙoƙarin gano matar domin kare wasu mata daga faɗawa a tarkonta, ya bayyana cewa matan nasa sun saba maganin na ruwa a wurin matar wanda suke haɗawa da madara, amma a wannan karon sai ta canza ta ba su na gari.
Shan kayan mata na daga cikin abubuwan da suka zama ruwan dare a tsakanin mata, inda masana kiwon lafiya ke gargaɗi game da haɗarinsi ga lafiyarsu da matucinsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Amarya Kayan Mata Maganin Gargajiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan
Tarayyar turai ta bayyana cewa ma’aikatan Agaji ba za su iya isha cikin garin Al-fahar ba,kuma birnin ya zama tamkar makabarta.
Tarayyar turai din ta bakin mai Magana da yawunta Eva Herneserova ta kuma ce; Sudan ta zama daya daga cikin kasashen da gudanar da ayyukan agaji ya tsananta a duniya,kuma har yanzu da akwai fararen hula da aka killace su adaidai lokacin da ake ci gaba da kai wa asibitoci hare-hare.
Eva Herneserova ta kuma ce; Babu sauki ko kadan a kokarin shiga cikin birnin domin isar da kayan agaji.
Ma Magana da yawun kungiyar tarayyar turai din ta kuma yi gagradi akan cewa bai kamata a rika amfani da yunwa da kuma kisan kiyashi a matsayin makamin yaki ba,domin hakan yana a matsayin take dokokin kasa da kasa ne na ayyukan agaji.
Haka nan kuma ta yi kira ga dukkanin bangarorin da suke fada da juna da koma kan teburin tattaunawa da kuma tsagaita wutar yaki.
Rundunar kai daukin gaggawa ta RSF kwace iko da birnin Al-fasha, bayan da killace shi na tsawon watanni 18. A yayin da mayana rundunar ta RSF su ka shiga cikin birnin sun aikata laifukan yaki da ya hada da yi wa fararen hula kisan kiyashi.
Bugu da kari, suna hana mutane ficewa daga cikin garin domin zuwa inda za su sami aminci.
Gwamnatin Sudan tana zargin kasar UAE da taimakawa mayakan na RSF da makamai da kuma kawo ‘yan ina da yaki daga kasashen Columbia, Sudan Ta Kudu da Afirka Ta Tsakiya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon November 7, 2025 Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza November 7, 2025 Falasdinawa Miliyan 1.5 Ne Ke Cikin Mawuyacin Hali November 7, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya November 7, 2025 Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar November 7, 2025 An Rantsar Da Paul Biya A Matsayin Shugaban Kamaru Karo Na Takwas November 7, 2025 Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar November 7, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jinin Isra’ila . November 7, 2025 Pezeshkiyan: Masu Kawo Rarraba Tsakanin Musulmi Suna yi wa Yan Sahayuniya Aiki Ne November 7, 2025 Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar November 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci