An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’
Published: 8th, May 2025 GMT
An kwantar da wasu matan aure kishiyoyin juna a asibiti bayan da suka sha maganin kara sha’awa domin burge mijinsu bayan ya auro mata ta uku.
Kishiyoyin biyu da ke yankin Dakwa a Abuja sun sha maganin gargajiyan, wanda aka fi sani da kayan mata ne, kwana uku bayan amaryar da mijinsu ya auro ta tare.
Da take tabbatar da faruwar lamarin, mijin nasu ya ce bayan kai su asibiti ne aka yi musu gwaji aka gano cewa wasu gaɓoɓinsu sun samu matsala, wanda ake zargin maganin da suka sha ne ya haddasa.
Ya ce, “ina gidan amarya aka kira ni cewa matana ba su da lafiya, inda na je na samu suna birgima cewa cikinsu na ciwo. Sai na kira wata nas ta duba su ta su magani ta yi musu ƙarin ruwa amma basu sani ba.
“Shi ne sai da muka kai su asibitin Madallah da ke Jihar Neja.
“A nan ne aka yi musu gwaji aka gano cewa wasu gaɓoɓinsu sun samu matsala, aka yi musu aiki,” in ji shi.
Magidancin mai suna Musa Muhammad ya bayyana cewa sallamo matan nasa a ranar Litinin, kuma an gano cewa sun sayi kayan matan ne a wajen wata wata mai tallar maganin gargajiya da suka saba saya.
Magidancin wanda ya ce yana ƙoƙarin gano matar domin kare wasu mata daga faɗawa a tarkonta, ya bayyana cewa matan nasa sun saba maganin na ruwa a wurin matar wanda suke haɗawa da madara, amma a wannan karon sai ta canza ta ba su na gari.
Shan kayan mata na daga cikin abubuwan da suka zama ruwan dare a tsakanin mata, inda masana kiwon lafiya ke gargaɗi game da haɗarinsi ga lafiyarsu da matucinsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Amarya Kayan Mata Maganin Gargajiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin HKI Sun Rushe Gidajen Falasdinawa Fiye Da 100 A Yammacin Kogin Jordan
A cikin wata daya kadai sojojin HKI sun rushe gidajen Falasdinawa 152 a yammacin Kogin Jordan.
Majiyar Falasdinawa ta ambaci cewa a kudancin garin Khalil ‘yan mamayar sun rushe gidaje 25 da kuma wasu cibiyoyi, da hakan ya sa adadin gidajen da su ka rushe zuwa 152 kamar yadda hukumar Falasdinu ta ambata.
Bugu da kari, majiyar Falasdinawan ta ce, ‘yan mamayar sun kuma aike wa da wasu cibiyoyin da gidaje 46 gargadin cewa za su rushe su, da yin kira da su fice daga cikinsu.
Wata cibiyar ta Falasdinawa ta ce fada wa kamfanin dillancin labarun “Anatoli’ cewa; ;yan mamayar sun rushe gidaje 96 da mutane suke rayuwa a cikinsu, sai kuma wasu gidaje 10 da babu mutane a ciki.Haka nan kuma rusau din ya shafi wasu cibiyoyin noma 34.
Mafi yawancin gidajen da aka rushe dai suna a yankin Tubas ne, Khalil sannan kuma da birnin Kudus.
Wani rahoto ya ambaci cewa; A cikin watan da ya gabata,’yan mamaya suna nazarin gina matsugunan ‘ya share wuri zauna 27 a cikin birnin Kudus.
A gefe daya, ‘yan share wuri zauna din sun kai hare-hare akan Falasdinawa har sau 1693 wanda ya fara a cikin watan Afrilu. Hare-haren kuwa sun hada lalata hanyoyi da tunbuke bishiyoyi, a kwace filayen Falasdinawa.