An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’
Published: 8th, May 2025 GMT
An kwantar da wasu matan aure kishiyoyin juna a asibiti bayan da suka sha maganin kara sha’awa domin burge mijinsu bayan ya auro mata ta uku.
Kishiyoyin biyu da ke yankin Dakwa a Abuja sun sha maganin gargajiyan, wanda aka fi sani da kayan mata ne, kwana uku bayan amaryar da mijinsu ya auro ta tare.
Da take tabbatar da faruwar lamarin, mijin nasu ya ce bayan kai su asibiti ne aka yi musu gwaji aka gano cewa wasu gaɓoɓinsu sun samu matsala, wanda ake zargin maganin da suka sha ne ya haddasa.
Ya ce, “ina gidan amarya aka kira ni cewa matana ba su da lafiya, inda na je na samu suna birgima cewa cikinsu na ciwo. Sai na kira wata nas ta duba su ta su magani ta yi musu ƙarin ruwa amma basu sani ba.
“Shi ne sai da muka kai su asibitin Madallah da ke Jihar Neja.
“A nan ne aka yi musu gwaji aka gano cewa wasu gaɓoɓinsu sun samu matsala, aka yi musu aiki,” in ji shi.
Magidancin mai suna Musa Muhammad ya bayyana cewa sallamo matan nasa a ranar Litinin, kuma an gano cewa sun sayi kayan matan ne a wajen wata wata mai tallar maganin gargajiya da suka saba saya.
Magidancin wanda ya ce yana ƙoƙarin gano matar domin kare wasu mata daga faɗawa a tarkonta, ya bayyana cewa matan nasa sun saba maganin na ruwa a wurin matar wanda suke haɗawa da madara, amma a wannan karon sai ta canza ta ba su na gari.
Shan kayan mata na daga cikin abubuwan da suka zama ruwan dare a tsakanin mata, inda masana kiwon lafiya ke gargaɗi game da haɗarinsi ga lafiyarsu da matucinsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Amarya Kayan Mata Maganin Gargajiya
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
Shugaban Ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta ci gaba da mayar da martani kan hare-haren da Isra’ila ke kai mata.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake magana da shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ta wayar tarho.
Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a BornoShugaba Pezeshkian ya ce Iran tana da niyyar yin haɗin gwiwa da sauran ƙasashe don amfani da makamashin nukiliya ta hanyar da ba ta da alaƙa da yaƙi, amma hakan ba yana nufin za su dakatar da inganta shirye-shiryensu na nukiliya gaba ɗaya ba.
Ya ƙara da cewa hare-haren da Isra’ila ke kai wa ƙasarsa ba za su wuce haka nan ba, domin kuwa Iran za ta riƙa mayar da martani mai zafi.
A ranar Asabar, rundunar sojin Iran ta yi gargaɗi cewa za ta kai wa Isra’ila ta hark ta jiragen ruwa.
A cewar wani kakakin rundunar sojin Iran da ya bayyana a wani bidiyo, duk ƙasar da ta tura makamai zuwa Isra’ila, kamar ta shiga yaƙi da Iran ce kai-tsaye, kuma Iran ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen kare kanta ba.
A ranar Juma’ar da ta gabata, Iran ta harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa zuwa Isra’ila, lamarin da ya jikkata mutane aƙalla 19 a birnin Haifa da ke Arewacin Isra’ila, kamar yadda wani asibiti a yankin ya tabbatar.