Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Waya

এছাড়াও পড়ুন:

Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ce ba gazawa ba ce ta sa ta yanke shawarar tattaunawa da ’yan bindigar da suka yanke hukuncin ajiye makamansu ba.

Ta ce wannan hanya ce mafi kyau da za ta kawo zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya Kotu ta daure mutumin da yake yada bidiyon tsiraici shekara 76 a kurkuku

Wani mai amfani da kafar sada zumunta, Basharu Altine Guyawa, ya soki wannan mataki na gwamnatin.

Amma Mai Bai Wa Gwamnan Jihar Shawara kan Tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ya ce manufar gwamnati ita ce ta kawo zaman lafiya, ba don ta kasa ba.

Ya ce, “Mun san kowa na da ‘yancin faɗin albarkacin bakinsa. Amma dole ne mu fayyace dalilin da ya sa Gwamna Ahmed Aliyu ke amfani da hanyoyi daban-daban wajen magance matsalar rashin tsaro, ciki har da tattaunawa da ‘yan bindigar da suka tuba.”

Ya ƙara da cewa abin mamaki ne yadda Guyawa ke sukar wannan yunƙuri.

Ya ce shi ma ya taɓa buƙatar shirin shiga tsakanin gwamnati da ‘yan bindiga domin yin sulhu.

Kanal Usman ya bayyana cewa gwamnati tana amfani da dukkanin matakai biyu; na ƙarfi da na sulhu.

A cewarsa, mutane da yawa a Rabah, Goronyo, Isa, Sabon Birni da wasu yankuna na ta yin hijira.

Manoma sun bar gonakinsu, amfanin gona ya ragu, kuma kasuwanci ya tsaya cak.

Wannan ya jawo ƙarancin abinci da tsadar rayuwa a faɗin jihar.

“Burinmu shi ne mu dawo da zaman lafiya, mu dawo da mutane gidajensu, sannan a sake farfaɗo da harkokin noma da kasuwanci,” in ji shi.

Ya ce har yanzu gwamnati na aike jami’an tsaro inda ya dace.

Amma waɗanda suka tuba da gaske za a karɓe su bisa kulawa da tsari na gyaran hali.

“Wannan ba gajiyawa ba ce ko jin tsoro, wannan dabara ce ta sulhu domin ɗorewar zaman lafiya.”

Amma ya roƙi masu sukar gwamnati da su yi magana cikin hankali.

“Jihar Sakkwato na buƙatar haɗin kai da mafita, ba rabuwar kai da zargi ba. Gwamna Ahmed Aliyu na aiki tuƙuru don kawo zaman lafiya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
  • Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano
  • CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 
  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna
  • Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5
  • Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano
  • Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto
  • Ɗan TikTok Tsulange Ya Shiga Hannu Bisa Wanka Da Rigar Mama A Titi