A cewar sa, wannan bita tana da nufin tantance yadda aka samu cigaba a aiki, da kuma tabbatar da cewa hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar suna tafiya daidai da abin da aka ɗora masu a matsayin nauyi.

 

Ya ce: “Muna nan ne don sauraron shugabannin hukumomi domin mu ga yadda suka aiwatar da muhimman abubuwan da muka rattaba hannu a kai.

Idan akwai ƙalubale, za mu tattauna su. Idan akwai cikas, za mu duba abin da za mu iya yi domin shawo kansu.”

 

Ministan ya bayyana wannan taro a matsayin hanyar tantance kai kafin a kai tsakiyar wa’adin gwamnatin yanzu.

 

Ya ce: “Ku tuna cewa wannan gwamnati ta fara aiki kusan shekaru biyu da suka gabata. Cikin ƙasa da wata guda daga yanzu, wannan gwamnati za ta kai rabin wa’adin ta a ranar 29 ga Mayu.

 

“Saboda haka, lokaci ya yi – kamar yadda Ofishin Shugaban Ƙasa ya nema – da kowace ma’aikata za ta fidda sakamakon aikin ta kan abubuwan da ta tsara kuma aka amince da su ta hannun ofishin CDCU da ke Ofishin Shugaban Ƙasa.”

 

Idris ya kuma jaddada cewa ma’aikatar sa na jajircewa wajen samar wa ‘yan Nijeriya da sahihan bayanai game da nasarorin gwamnati da kuma ƙalubalen da take fuskanta.

 

Ya ce: “Abin da wannan ma’aikatar ke yi shi ne tabbatar da cewa ba wai kawai muna wayar da kan ‘yan Nijeriya kan abubuwan da ke cikin hangen nesa na Shugaban Ƙasa ba, har ma muna bayyana ƙalubalen da ke akwai cikin gaskiya da riƙon amana? Tabbas, wannan ne abin da muka ɗauka tun farko kuma za mu ci gaba da bin wannan hanya.”

 

Ya ƙara da cewa babban aikin ma’aikatar shi ne tsarawa da aiwatar da dabarun sadarwa masu ma’ana domin inganta gaskiya da rarraba bayanai game da manufofi da shirye-shiryen gwamnati, yaƙi da yaɗa ƙarya, da kuma ƙarfafa wayar da kan ‘yan ƙasa bisa fifikon gwamnatin Tinubu.

 

Taron ya samu halartar shugabannin hukumomi kamar haka: Darakta Janar na Hukumar Talabijin ta Nijeriya (NTA), Kwamared Abdulhamid Dembos; Darakta Janar na Hukumar Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Dakta Mohammed Bulama; Darakta Janar na Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA), Mista Lanre Issa Onilu; Darakta Janar na Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC), Mista Charles Ebuebu; Darakta Janar na Muryar Nijeriya (VON), Malam Jibrin Baba Ndace; Darakta Janar na Hukumar Kula da Tallace-tallace (ARCON), Dakta Olalekan Fadolapo; da Manajan Darakta na Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), Malam Ali M. Ali.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Darakta Janar na Hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

A ranar Juma’ar da ta gabata ne, Trump ya sake mayar da Nijeriya matsayin kasa mai matukar damuwa, sannan ya yi gargadin cewa; “idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bayar da izinin kashe kiristoci, nan take Amurka za ta dakatar da duk wani taimako da take bai wa Nijeriya, sannan kuma mai yiwuwa ta shiga kasar, domin kakkabe ‘yan ta’addan Islama da ke aikata wadannan munanan ayyuka na ta’addanci.”

Kazalika, ya kuma umarci Ma’aikatar Yakin Amurka, da ta shirya domin daukar mataki.

Pete Hegseth, Sakataren Yakin Amurka, a ranar Asabar ya ce; Ma’aikatar Yaki na shirin daukar mataki.

Barazanar Trump dai, ta biyo bayan zargin da wani dan majalisar dokokin Amurka, Ted Cruz, ya yi a shafinsa na D, a ranar 7 ga watan Oktoba na cewa; an kashe kimanin kiristoci 50,000, tun daga shekarar 2009 tare da lalata makarantu 2,000 da rusa Coci-coci 18,000, wanda musulmi masu dauke da makamai suka dauki nauyin aikatawa. Sai dai Cruz, bai ambaci tushen bayanan nasa ba.

A martanin da ya mayar, Shugaba Bola Ahmed Tinubu, a ranar Asabar da ta gabata, ya yi watsi da zargin da Trump ya yi wa Nijeriya, yana mai dagewa kan cewa; kasar ta ci gaba da kasancewa a matsayin dimokuradiyya mai tushe da tsarin mulkin kasar ya ba da ‘yancin yin addini.

A cewarsa, Nijeriya ta tsaya tsayin daka a matsayin dimokuradiyyar da kundin tsarin mulki ya ba da ‘yancin walwala.

Ya ce, tun daga shekarar 2023, gwamnatinsa ta ci gaba da kasancewa tare da shugabannin Kiristoci da na Musulmi baki-daya, sannan kuma tana ci gaba da magance matsalolin tsaro da suka shafi ‘yan kasa a fadin addinai da yankuna daban-daban.

“Yancin addini da juriya, sun kasance ginshikin tushenmu, kuma za su ci gaba da kasancewa a haka, Nijeriya na adawa da zalincin addini, sannan kuma ko kadan ba ta karfafe shi ba.

“Nijeriya kasa ce da kundin tsarin mulkinta ya bayar da tabbacin kare ‘yan kasa a kowane addini.

Gwamnatinmu, ta kudiri aniyar yin aiki tare da gwamnatin Amurka da sauran kasashen duniya, domin zurfafa fahimta da hadin gwiwa, kan kare al’ummomin dukkanin addinai,” in ji Tinubu.

Ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya, a wata sanarwa da kakakinta, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, ya fitar a ranar Asabar ya ce: “Gwamnatin Tarayyar Nijeriya, ta lura da kalaman da shugaban kasar Amurka Donald J. Trump, ya yi a baya-bayan nan, game da kashe-kashen kiristoci da ake yi a Nijeriya tare da yin kira da a ayyana kasar a matsayin “Kasar da za a mayar da hankali a kai.”

“Yayin da Nijeriya ta yaba da damuwar duniya game da ‘yancin Dan’adam da ’yancin addini, wadannan ikirari, ba su nuna halin da ake ciki a kasar ba, ‘yan Nijeriya na dukkanin addinai, sun dade suna rayuwa tare, suna yin aiki tare, sannan kuma suna yin ibada tare a cikin lumana.

“A karkashin jagorancin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, Nijeriya ta jajirce wajen yaki da ta’addanci, karfafa hadin kan addinai da kare rayuka da ‘yancin al’ummarta.

“Nijeriya za ta ci gaba da yin aiki tare da gwamnatin Amurka, don zurfafa fahimtar juna game da yanayin yankin da kuma kokarin da ake yi na zaman lafiya da tsaro.”

 

Su Ma Musulmin Ana Kashe Su- Yankin Middle Belt

Shugaban Kungiyar ‘Middle Belt’ (MBF), Dakta Bitrus Pogu, ya bayyana cewa; ‘yan ta’addan kasar nan ne suke kashe musulmai kamar yadda suke kashe Kiristoci.

Ya ce, barazanar da Amurka ta yi, kira ne kawai na farkar da gwamnatin Nijeriyar, domin murkushe ‘yan ta’adda.

Ya kara da cewa; “Amurka ba ta fitar da wata barazanar daukar matakin soji ba, illa kawai ta sanya Nijeriya a matsayin kasa wadda ya kamata a sanya wa ido.

“Hakan yana nufin sanya takunkumi, shiga tsakani don tabbatar da cewa; an tilasta wa gwamnati yin abin da ya dace, sannan kuma; idan har za a dauki wani mataki na soja, wato na fatattakar ‘yan tada kayar baya, ba za a zama kasa daya ba, kana kuma; hakan zai faru ne kawai idan kasarmu ta ki yin abin da ya kamata ta yi.

“Haka zalika, a koda-yaushe na sha fadin cewa; sojojinmu na kokari kwarai da gaske, amma akwai masu zagon kasa a cikin jami’an tsaron, kuma daga lokaci zuwa lokaci, an yi ta samun hakan kamar a zamanin marigayi Buhari.

“Ana kashe mutane daruruwa babu wanda ya damu, sannan babu wanda aka kama a tsakanin mutanen da suke kai wannan hari, wadannan mutane za su zo su kai hari, amma har sai an bai wa sojoji umarni kafin su yi wani abu a kai ana ji ana kallo.

“Don haka, batu na gaskiya akwai matsala, sannan abin takaici kuma shi ne, duk wadannan kungiyoyi masu tayar da kayar baya a Arewa, suna kashe Kiristoci ne da kuma Musulmai, kana kuma suna kiran kungiyarsu da ta jihadi, wadanda a zahiri ba Musulmai ba ne.

 

Kungiyar ACF Ta Musanta Zargin Kisan Kiristoci Kadai

Kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF), a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadin da ta gabata, ta hannun sakataren yada labaranta na kasa, Farfesa Tukur Muhammad-Baba, ta yi gargadi game da mamayar da kasashen waje ke yi wa wata kasa mai cin gashin kanta ta Amurka.

ACF ta kuma yi nuni da cewa, ‘yan ta’adda a kasar nan, na kashe ‘yan Nijeriya daga kowane irin addini.

“Tare da dimbin bayanan sirrin da aka tura ko’ina, ya kamata a ce, Amurka ta fi kowa sanin halin da ake ciki na kisan da ake yi.

“Kamar sauran ‘yan Nijeriya masu kishin kasa, mambobin kungiyar tuntuba ta Arewa, sun samu labari mai cike da takaici game da ayyana Nijeriya a matsayin kasar da Amurka ta sanya wa ido,” in ji shi.

“Tuni dai ‘yan Nijeriya na kowane bangare na fama da hare-haren da wasu bata gari da suka hada da ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga, ‘yan tada kayar baya da masu tsattsauran ra’ayin addini a yankin Arewa maso Gabas, Arewa ta Tsakiya, Arewa maso Yamma, Kudu maso Gabas da sauran sassan kasar nan.

Ya kara da cewa “Shekaru da dama, kungiyar ACF na sane da cewa; gwamnatocin Nijeriya da suka biyo baya, sun roki Amurka da ta taimaka musu ba tare da wata fa’ida ba.”

Ya ce, duk wani tallafi daga kasashen waje ya kamata ya mayar da hankali wajen taimakawa sojojin Nijeriya, maimakon kai hari kan wata kungiyar addini.

Haka zalika, ACF ta gargadi ‘yan Nijeriya da su tuna da darussan tarihi, inda ta ambaci tsoma bakin da aka yi a Bietnam, Afghanistan, Syria, Irak da kuma kusa da gida, akwai Libya da Sudan, da kasashen Sahelian, har sai sun sake tunani, don lissafta wasu kadan.

Taron ya yi maraba da martanin da gwamnatin tarayya ta bayar, inda ta bayyana cewa; ya cancanci goyon bayan duk wanda abin ya shafa.

ACF ta kuma bukaci ‘yan Nijeriya da su yi tunani mai zurfi game da lamarin tare da marawa gwamnati baya, yayin da take mayar da martani kan lamarin, sannan ta yi kira ga hadin kan yankin daga “Afirka da sauran kasashe.”

A cewar sanarwar: “Bisa la’akari da babban tasiri ga aikin Nijeriya, ACF za ta ci gaba da sa ido, tantancewa da kuma mayar da martani ga ci gaban al’amarin.”

Har ila yau, shugabannin addinai daban-daban a fadin wadannan kasa tare kuma da wasu jiga-jigai a fannin siyasa da sarakuna, sun yi watsi da wannan zargi na Kasar Amurka tare da barazanar da suka yi na kawo wa Nijeriya hari.

Baya ga watsi da wannan barazana da Trump ya yi, Rabaran John Joseph Hayab, ya yi kira ga Kiristoci da Musulmi daga Arewacin Nijeriya da su gudanar da tarukan hadin kai da zaman lafiya.

Rabaran Hayab, wanda shi ne Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN), na Jihohin Arewa 19 da kuma Babban Birnin Tarayya (FCT), ya ci gaba da ba da shawarar a rika tattaunawa tsakanin addinai, domin magance matsalolin da yankin ke fuskanta, kamar rashin tsaro da kuma rashin yarda da juna.

Haka nan, malaman addinin musulinci, kamar irin su Sheikh Ahamad Gumi, Sheikh Ibrahim Makari, Sarkin musulmi da sauran ‘yan siyasa kamar irin su Sanata Rabi’u Kwankwaso, Sanata Shehu Sani da Manjo Hamza Almustapha, sun yi kakkausan martani a kan wannan barazana da Kasar Amurka ta yi.

A ranar Talatar da ta gabata ne, Kasar Sin; ita ma ta shiga jerin cikin wadanda suka yi watsi da barazanar da Amurkan ta yi, na daukar matakin soji kan Nijeriya, tana mai cewa; tana matukar adawa da duk wani katsalanda daga waje a cikin harkokin cikin gidan kasar.

Matsayin gwamnatin kasar ta Sin, ya zo ne a ranar da gwamnatin tarayya ta ce; masu tsattsauran ra’ayin addini ne ke bayan wannan labari na zargin kisan kiyashi da ake yi wa Kiristoci, tare da cewa; babban burinsu shi ne, raba kan al’umma.

Ita ma a nata bangaren, Majalisar Dinkin Duniya; ta yi kira ga kasashe da su guji amfani da karfi, dangane da barazanar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa Nijeriya, kan zargin kisan kiyashi da aka ce ana yi wa Kiristoci.

Har ila yau, a cikin jawabai daban-daban, Kungiyar Tarayyar Turai (EU) da Kungiyar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), sun yi gargadi kan ayyukan da za su iya yi wa Nijeriya zagon kasa, inda suka dage cewa; ta’addanci a yankin ya shafi dukkanin mabiya addinan guda biyu.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari  November 7, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT November 6, 2025 Manyan Labarai Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya  November 6, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar Najeriya
  • Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
  • Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano