Aminiya:
2025-11-27@23:12:16 GMT

‘Yan sanda sun bankaɗo masana’antar man gyaɗa na bogi a Kaduna

Published: 8th, May 2025 GMT

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta bankaɗo wata haramtacciyar masana’antar man gyaɗan bogi, tare da cafke mutane uku da ake zargin suna da hannu a harkar.

Wannan samame da jami’an sashen leƙen asiri na rundunar suka gudanar ƙarƙashin jagorancin SP Sani Bello, ya gudana ne da misalin ƙarfe 11:00 na safiyar ranar 5 ga Mayu bayan samun bayanan sirri.

An gabatar da sabbin shaidu kan Nnamdi Kanu Mazauna gari sun kori Boko Haram bayan kashe kyaftin ɗin soja

An gano haramtacciyar masana’antar ce a wani fili da aka kewaye da katanga a titin Mamadi, a yankin Maraban Jos da ke Kaduna.

Mai magana da yawun ‘yan sanda na jihar, DSP Mansir Hassan, shi ne ya fitar da sanarwar a madadin Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Rabiu Muhammad, a ranar Laraba.

Ya bayyana cewa waɗanda aka kama a masana’antar sun haɗa da Zailani Shuaibu, mai shekaru 33, wanda ake zargin shine mamallakinta, da Nasiru Usman mai shekaru 24, da kuma Salisu Usman mai shekaru 49 – dukkansu mazauna Maraban Jos ne.

A cewarsa, ‘yan sanda sun samu ganguna biyu maƙare da kayan aikin sarrafa man, da jarkoki goma sha biyar masu nauyin lita 25 na man da ba a kammala tacewa ba, sai jarkoki biyu da ke ɗauke da man gyaɗa na bogi da aka gama tacewa, da kuma ganga guda mai kyau.

DSP Hassan ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar ya jaddada ƙudirin rundunar na kare lafiyar jama’a da kuma kawar da ayyukan laifi a cikin al’umma.

Haka kuma, ya buƙaci mazauna da su ci gaba da lura da abin da ke faruwa a yankunansu domin kai rahoton motsin da ba su gamsu da shi ba zuwa ofishin ‘yan sanda mafi kusa da su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan sanda a Kaduna masana antar

এছাড়াও পড়ুন:

An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya

Sufeto Janar na ’Yan sandan Nijeriya, Olukayode Egbetokun, ya sanar da cewa sun aiwatar da umarnin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na janye dakarunsu daga gadin ɗaiɗaikun mutane da ake kira VIP.

IG Egbetokun ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai a yau Alhamis, yana mai cewa zuwa yanzu sun janye dakaru 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya.

Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da Olympiacos An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji

“Wannan karon za mu aiwatar da umarnin da kyau saboda umarnin shugaban ƙasa ne,” in ji shi.

“Babu wani gwamna, ko minista, ko abokaina da za su kira su takura min saboda sun san cewa umarnin shugaban ƙasa ne. Ina kuma da tabbacin cewa ba za su uzzura wa kwamashinonin ’yan sanda ba ma.”

Ya ƙara da cewa za su tura jami’an da aka janye zuwa “wuraren da aka fi buƙatarsu, musamman a wannan lokaci mai muhimmanci.”

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da aika ’yan sanda ga manyan mutane domin ba su tsaro na musamman, yana mai mayar da su zuwa aikin tsaro da ya shafi al’umma baki ɗaya.

Kazalila, a ranar Laraba, 26 ga watan Nuwamba ne Tinubun ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a faɗin ƙasar, inda ya bayar da umarnin a ɗauki matakan gaggawa domin magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.

Shugaban ya ce a ɗauki sababbin ’yan sanda 20,000, ƙari a kan guda 30,000 da ya fara amincewa a ɗauk, wanda za a yi amfani da sansanonin horar da masu yi wa ƙasa hidima wajen horar da sababbin ’yan sandan da za a ɗauka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe