Aminiya:
2025-06-23@22:53:47 GMT

‘Yan sanda sun bankaɗo masana’antar man gyaɗa na bogi a Kaduna

Published: 8th, May 2025 GMT

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta bankaɗo wata haramtacciyar masana’antar man gyaɗan bogi, tare da cafke mutane uku da ake zargin suna da hannu a harkar.

Wannan samame da jami’an sashen leƙen asiri na rundunar suka gudanar ƙarƙashin jagorancin SP Sani Bello, ya gudana ne da misalin ƙarfe 11:00 na safiyar ranar 5 ga Mayu bayan samun bayanan sirri.

An gabatar da sabbin shaidu kan Nnamdi Kanu Mazauna gari sun kori Boko Haram bayan kashe kyaftin ɗin soja

An gano haramtacciyar masana’antar ce a wani fili da aka kewaye da katanga a titin Mamadi, a yankin Maraban Jos da ke Kaduna.

Mai magana da yawun ‘yan sanda na jihar, DSP Mansir Hassan, shi ne ya fitar da sanarwar a madadin Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Rabiu Muhammad, a ranar Laraba.

Ya bayyana cewa waɗanda aka kama a masana’antar sun haɗa da Zailani Shuaibu, mai shekaru 33, wanda ake zargin shine mamallakinta, da Nasiru Usman mai shekaru 24, da kuma Salisu Usman mai shekaru 49 – dukkansu mazauna Maraban Jos ne.

A cewarsa, ‘yan sanda sun samu ganguna biyu maƙare da kayan aikin sarrafa man, da jarkoki goma sha biyar masu nauyin lita 25 na man da ba a kammala tacewa ba, sai jarkoki biyu da ke ɗauke da man gyaɗa na bogi da aka gama tacewa, da kuma ganga guda mai kyau.

DSP Hassan ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar ya jaddada ƙudirin rundunar na kare lafiyar jama’a da kuma kawar da ayyukan laifi a cikin al’umma.

Haka kuma, ya buƙaci mazauna da su ci gaba da lura da abin da ke faruwa a yankunansu domin kai rahoton motsin da ba su gamsu da shi ba zuwa ofishin ‘yan sanda mafi kusa da su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan sanda a Kaduna masana antar

এছাড়াও পড়ুন:

Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya aike da saƙon ta’aziyyarsa ga iyalan matafiyan da aka kashe a garin Mangu na Jihar Filato, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure.

A yayin isar da saƙon a ƙauyen DanBami da ke Anguwar Rimi, a Ƙaramar Hukumar Kudan, Gwamnan ya roƙi Allah Ya gafarta wa mamatan tare da addu’a ga waɗanda suka ji rauni.

An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

Gwamnan, wanda Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kaduna, CP Rabi’u Muhammad, ya wakilta, ya ce gwamnati na ƙoƙarin gano waɗanda suka aikata wannan mummunan aiki.

Ya tabbatar da cewa ana ci gaba da tuntuɓar Gwamnan Jihar Filato domin ɗaukar matakan da suka dace.

An tabbatar da cewa mutum 11 daga cikin 31 da ke cikin mota sun rasu, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa bikin ɗaurin auren wani ɗan uwansu a Mangu.

Mutum na 12 shi ne direban motar wanda ɗan asalin garin Basawa ne.

Gwamna Uba Sani, ya ce an kama wasu mutane da ake zargi da hannu a lamarin, kuma gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin an hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.

Ya kuma roƙi al’umma, musamman matasa, da su guji ɗaukar hukunci a hannunsu, domin gwamnati na aiki kafaɗa da kafaɗa da Jihar Filato domin tabbatar da adalci.

“Na jajanta wa iyalan mamatan bisa wannan babban rashi. Ina roƙon ku da ku ɗauki wannan a matsayin ƙaddara. Mutuwa abu ne da babu makawa, kuma kowa zai fuskance ta a lokacin da Allah Ya rubuta masa,” in ji Gwamnan.

A nasa ɓangaren, Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, wanda Hakimin Basawa, Haruna Abubakar, ya wakilta, ya roƙi Allah Ya jiƙan mamatan tare da bai wa iyalansu haƙuri da juriya.

Malam Musa Ibrahim, da ya yi magana a madadin iyalan mamatan da al’ummar DanBami, ya ce sun rungumi ƙaddara bisa wannan al’amari.

Sai dai ya roƙi Gwamnan da ya tallafa wa iyalan ta hanyar biyansu diyya domin rage musu raɗaɗin rashin da suka yi.

Ya ce dukkanin mamatan ‘yan garin ne kuma ‘yan uwan juna ne, direban motar ne kawai daga garin Basawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matashi ya yi wa maraya ɗan shekara 10 kisan gilla a Zariya
  • Matsayi ya yi maraya ɗan shekara 10 kisan gilla a Zariya
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe
  • Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
  • Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan
  • An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna
  • Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato
  • Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda