Sumaila, tsohon mataimaki na musamman ga shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harkokin majalisar dokokin kasar, ya bayyana jam’iyyar NNPP a matsayin “jam’iyyar da ke da rabe-rabe da tabarbarewar al’amura, inda ya ce, rikicin da ya dabaibaye Jam’iyyar a fili yake babu mai musantawa, wadanda suka hada da shari’o’i a kotuna da dama da kuma gwagwarmayar shugabancin jam’iyyar.

 

A karshe, Sumaila ya kafa uzuri a karkashin doka ta 42, inda ya bayyana godiyarsa ga takwarorinsa da jama’ar mazabarsa, inda ya yi alkawarin kara zage damtse wajen gudanar da ayyukansa na ‘yan majalisu domin yi wa kasa hidima.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

Aƙalla mutum 10 ne suka rasu a daren ranar Juma’a bayan wani ɗan ƙunar baƙin wake ya kai hari da bam a wani wsjen cin abinci da ke garin Konduga, a Jihar Borno.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Borno, ASP Nahum Daso, ya tabbatar da faruwar lamarin.

’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano

Ya ce jami’an tsaro da suka haɗa da ‘yan sanda da sojoji na gudanar da bincike domin gano haƙiƙanin abin da ya faru da kuma adadin waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Ya ce, “Wani mutum ya kutsa cikin taron mutane da misalin ƙarfe 10 na dare tare da bam, wanda ya tarwatsa kansa kuma ya kashe sama da mutum 10.”

Wani masani kan ta’addanci, Zagazola Makama, ya bayyana cewa mutum 24 ne, suka rasu a sanadin harin, inda ya ce mace ce ta kai harin ƙunar baƙin waken.

Ya ƙara da cewa fashewar ta yi tsanani wanda sai kan matar aka samu.

Bayan harin, an tura tawagar sojoji, ƙwararrun masu binciken bam na ‘yan sanda, ’yan sa-kai, da ƙungiyar CJTF zuwa wajen.

Sun yi bincike amma ba su samu bam na biyu a wajen ba.

An kwashe waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH) domin a kula da su.

An kai gawarwakin waɗanda suka rasu zuwa asibitin kuma likitoci sun tabbatar da rasuwarsu.

Makama, ya ce ana ci gaba da tantance sunayen waɗanda abin ya rutsa da su domin a miƙa gawarwakinsu ga iyalansu domin yi musu jana’iza.

Kai harin ƙunar baƙin wake na ɗaya daga cikin dabarun da ƙungiyar Boko Haram ta fara amfani da su a farko-farkon fara ta’addancinta a Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?
  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
  • CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 
  • Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno
  • Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa
  • Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
  • Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
  • Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’