HausaTv:
2025-11-08@20:14:11 GMT

Jagora: Muhimmin Aikin Makarantar “Hauza” Shi ne Isar Da Sakon Addini

Published: 7th, May 2025 GMT

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei wanda ya aike da sako zuwa wurin taron tunawa da cikar  shekara 100 daga kafuwar cibiyar koyar da addinin musulunci ta “Hauza” wanda aka yi a yau a birnin Kum, anan Iran, ya bayyana cewa: Aiki mafi muhimmanci na makarantar addini shi ne isar da sakon addinin musulunci domin gina sabon ci gaba na addinin musulunci.

Jagoran juyin musuluncin na Iran ya kuma bayyana cewa da akwai ayyuka masu yawa da suke na cibiyar koyar da addinin musulunci ta Hauza ne da sun kunshi bayar da jawabi akan sabbin batutuwa na zamani da suke bijirowa,  ruhin ci gaba, tsarkake zukata, da kuma siffa ta juyin juya hali.”

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma bayyana cewa daga cikin ayyukan cibiyar ilimin ta Hauza da akwai Shata muhimman layukan da za a gina ci gaban musulunci na zamani akansu, da kuma isar da sakwanninsa a cikin al’umma, kamar kuma yadda aikin Hauzar ne ta yi  tarbiyyar mutane su zama masana.

Tun da fari, Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya fara da bijiro da takaitaccen tarihin kafuwar cibiyar koyar da addinin musulunci ta Hauza a Kum, da rawar da Ayatullah Haj Sheikh Abdulkarim Ha’iri ya yi, har zuwa lokacin da ta rika bunkasa da ci gaba.

Jagoran juyin musuluncin na Iran ya bayyana Imam Khumaini ( q.s) a matsayin daya daga cikin malaman da Hauza ta haskaka da su, wanda ya yi nasarar kawo karshen tsarin sarauta na maha’inta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin November 8, 2025 Daga Birnin Sin CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin November 8, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong November 8, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne
  • Nigeria: Za A Ci Gaba Da Zaman Shari’ar Shugaban Kungiyar “IPOB” A ranar 20 Ga Watan Nan Na Nuwamba
  •  Lebanon: Mutane 2 Sun Jikkata Sanadiyyar Harin “Isra’ila” A Garin Bint-Jubail
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Tabbatar Da Hannun Amurka Wajen Kaddamar Da Yaki Kanta
  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  •  Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan
  • Yaduwar Juyin Mulki A Afirka
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini