HausaTv:
2025-09-24@14:05:43 GMT

Jagora: Muhimmin Aikin Makarantar “Hauza” Shi ne Isar Da Sakon Addini

Published: 7th, May 2025 GMT

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei wanda ya aike da sako zuwa wurin taron tunawa da cikar  shekara 100 daga kafuwar cibiyar koyar da addinin musulunci ta “Hauza” wanda aka yi a yau a birnin Kum, anan Iran, ya bayyana cewa: Aiki mafi muhimmanci na makarantar addini shi ne isar da sakon addinin musulunci domin gina sabon ci gaba na addinin musulunci.

Jagoran juyin musuluncin na Iran ya kuma bayyana cewa da akwai ayyuka masu yawa da suke na cibiyar koyar da addinin musulunci ta Hauza ne da sun kunshi bayar da jawabi akan sabbin batutuwa na zamani da suke bijirowa,  ruhin ci gaba, tsarkake zukata, da kuma siffa ta juyin juya hali.”

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma bayyana cewa daga cikin ayyukan cibiyar ilimin ta Hauza da akwai Shata muhimman layukan da za a gina ci gaban musulunci na zamani akansu, da kuma isar da sakwanninsa a cikin al’umma, kamar kuma yadda aikin Hauzar ne ta yi  tarbiyyar mutane su zama masana.

Tun da fari, Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya fara da bijiro da takaitaccen tarihin kafuwar cibiyar koyar da addinin musulunci ta Hauza a Kum, da rawar da Ayatullah Haj Sheikh Abdulkarim Ha’iri ya yi, har zuwa lokacin da ta rika bunkasa da ci gaba.

Jagoran juyin musuluncin na Iran ya bayyana Imam Khumaini ( q.s) a matsayin daya daga cikin malaman da Hauza ta haskaka da su, wanda ya yi nasarar kawo karshen tsarin sarauta na maha’inta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An ƙone al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi

Ana zargin wata matar aure, Rabi Nuhu da ke garin Magama Gumau a ƙaramar hukumar Toro ta Jihar Bauchi, da cin zarafin wata yarinya ’yar shekara biyar ta hanyar ƙone mata al’aura, saboda zargin tana yawan yin fitsarin kwance.

Wakilinmu ya gano cewa yarinyar marainiya ce wadda mahaifiyarta ta rasu kusan shekara ɗaya da ta gabata, inda take zaune tare da mahaifinta, Mohammed Umar, da matarsa.

CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100 Mahara sun kashe ɗan sanda sun ɗauke bindigarsa a Taraba

Wani mai fafutukar kare haƙƙin bil’adama a garin, Kabiru Abdulkadir, ya bayyana cewa sai bayan kwana biyar da ƙonewar ta faru ne al’amarin ya bayyana.

“Don guje wa matsala, mahaifin yarinyar ya sayi wata katifa ta daban domin ta riƙa kwanciya a kai, amma duk da haka matar tasa ba ta daina azabtar da yarinyar ba,” in ji Kabiru.

Aminiya ta ruwaito cewa, lamarin ya bayyana ne lokacin da yarinyar ta roƙi kawunta ya saya mata katifa, inda ta shaida masa cewa mamanta ta ƙona al’aurarta saboda yawan fitsarin kwance, dalili ke nan da ya yi wa ’yan sanda ƙorafi.

Kazalika, ana zargin cewa duk lokacin da matar ta samu sabani da mijinta, sai ta huce fushi a kan yarinyar.

Da yake jawabi, mahaifin yarinyar, Mohammed Umar, wanda ke aiki da wani gidan talabijin, ya tabbatar da cewa matarsa ta kan yi ƙorafi kan yawan fitsarin kwancen yarinyar, abin da ya sa ya saya mata katifa ta daban.

Umar ya ce: “A farko, da na ga ƙuna a jikinta, matata ta shaida min wai shayi mai zafi ne ya zubo a jikinta. A lokacin na gaskata hakan, har sai da na lura da ciwon yana ƙaruwa.”

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, CSP Mohammed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa rahoto ya iso ofishin su da misalin ƙarfe 3:00 na ranar 13 ga Satumba, 2025.

Wakil ya ce yarinyar ta sami ƙonuwa a ƙasan cikinta, cinyoyinta, da kuma al’aurarta.

Ya ƙara da cewa, kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Sani Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin a gaggauta kama matar tare da miƙa ta zuwa sashen manyan laifuka domin gudanar da cikakken bincike.

Ya bayyana cewa da zarar an kammala binciken, za a gurfanar da ita a gaban kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yada labaran karya a intanet babban laifi ne a Musulunci – Sheikh Ibrahim Khalil
  • Imam Khamenei: Hadin kan al’ummar Iran a yakin kwanaki 12 ya sanya makiya kunya
  • Jagora: Iran Ba Za Ta Taba Yin Watsi Da Inganta Sinadarin Uranium Ba
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • An ƙona al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • An ƙone al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • Kwamandan Sojan Iran: Ba Za Mu Taba Wasa Da Manufofinmu Na Kasa Ba
  • Jirgin Ruwan “Umar Mukhtar” Na Agaji Ya Kama Hanyar Zuwa Gaza Daga Kasar Libya
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Jinjinawa Tawagar Kokawar Greco-Roma Ta Iran Murnar Lashe Gasar Cin Kofin Duniya
  • APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027