HausaTv:
2025-05-08@11:43:54 GMT

“Amnesty International”: Korar Falasdinawa Daga Gaza Laifin Yaki Ne

Published: 7th, May 2025 GMT

A yau Laraba kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty Interantional” ta fitar da rahoto da a ciki ta yi kira ga HKI da ta kawo karshen shirinta na korar Falasdinawa daga Gaza da karfi, tare da cewa; Har yanzu Isra’ilan tana ci gaba da tafka laifukan yaki a Gaza da yi wa mutane kisan kiyashi.”

Haka nan kuma kungiyar kare hakkin bil’adaman ta kasa da kasa ta ce; Isra’ilan tana fakewa da batun fursunoni domin halartawa kanta aikata laifukan yaki akan Falasdinawa.

A wani rahoto na sirri da aka yi kwarmatonsa,an nuna yadda gwamnatin HKI ta amince da sake mamaye yankin zirin Gaza baki daya.

Tashar talabijin ta 12, ta ambata cewa Shirin wanda majalisar ministoci ta amince da shi, ya kunshi sake mamaye zirin  Gaza daga Arewacinsa zuwa kudancinsa.

A watan Febrairu ne dai shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi Magana akan Shirin fitar da Falasdinawa daga Gaza, da mayar da yankin zama wurin shakatawa.

A wancan lokacin dai kasashen duniya sun yi tir da furucin na Trump daga ciki har da kasashen turai abokan kawancen Amurka.

A halin yanzu dai HKI tana mamaye da kaso 1/3 na yankin Gaza, tare da rufe dukkanin kofofin shigar da tallafin abinci zuwa yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Tabbatar Da Ficewar Sanata Sumaila Daga NNPP Zuwa APC A Majalisa

Sumaila, tsohon mataimaki na musamman ga shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harkokin majalisar dokokin kasar, ya bayyana jam’iyyar NNPP a matsayin “jam’iyyar da ke da rabe-rabe da tabarbarewar al’amura, inda ya ce, rikicin da ya dabaibaye Jam’iyyar a fili yake babu mai musantawa, wadanda suka hada da shari’o’i a kotuna da dama da kuma gwagwarmayar shugabancin jam’iyyar.”

 

A karshe, Sumaila ya kafa uzuri a karkashin doka ta 42, inda ya bayyana godiyarsa ga takwarorinsa da jama’ar mazabarsa, inda ya yi alkawarin kara zage damtse wajen gudanar da ayyukansa na ‘yan majalisu domin yi wa kasa hidima.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Fara Gabatar Da Shirin “Kalaman Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Rasha
  • An Tabbatar Da Ficewar Sanata Sumaila Daga NNPP Zuwa APC A Majalisa
  • Jagora: Muhimmin Aikin Makarantar “Hauza” Shi ne Isar Da Sakon Addini
  •  Waji Jirgin Amurka Samfurin F-18 Na 3 Ya Fadi A Tekun “Red-Sea”
  • Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen Ta Sanar Da Cewa Ayyukan Yemen Na Tallafawa Gaza Ba Zai Tsayawa Ba
  • Birnin Kudu Za Ta Samar Da Cibiyar Horas Da Maniyata
  • Hamas : Tattaunawar sulhu ba ta da wani tasiri a halin da ake ciki
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa 50 A Yankin Zirin Gaza
  • PTAD Ta Dora Laifin Jinkirin Biyan Fansho Kan CBN, Ta Bukaci Hakuri