HausaTv:
2025-08-07@01:17:30 GMT

“Amnesty International”: Korar Falasdinawa Daga Gaza Laifin Yaki Ne

Published: 7th, May 2025 GMT

A yau Laraba kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty Interantional” ta fitar da rahoto da a ciki ta yi kira ga HKI da ta kawo karshen shirinta na korar Falasdinawa daga Gaza da karfi, tare da cewa; Har yanzu Isra’ilan tana ci gaba da tafka laifukan yaki a Gaza da yi wa mutane kisan kiyashi.”

Haka nan kuma kungiyar kare hakkin bil’adaman ta kasa da kasa ta ce; Isra’ilan tana fakewa da batun fursunoni domin halartawa kanta aikata laifukan yaki akan Falasdinawa.

A wani rahoto na sirri da aka yi kwarmatonsa,an nuna yadda gwamnatin HKI ta amince da sake mamaye yankin zirin Gaza baki daya.

Tashar talabijin ta 12, ta ambata cewa Shirin wanda majalisar ministoci ta amince da shi, ya kunshi sake mamaye zirin  Gaza daga Arewacinsa zuwa kudancinsa.

A watan Febrairu ne dai shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi Magana akan Shirin fitar da Falasdinawa daga Gaza, da mayar da yankin zama wurin shakatawa.

A wancan lokacin dai kasashen duniya sun yi tir da furucin na Trump daga ciki har da kasashen turai abokan kawancen Amurka.

A halin yanzu dai HKI tana mamaye da kaso 1/3 na yankin Gaza, tare da rufe dukkanin kofofin shigar da tallafin abinci zuwa yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon dan majalisa mai wakiltar mazabar tarayya ta Wukari/Ibi ta jihar Taraba a majalisar wakilai, Hon. Shiddi Danjuma Usman ya fice daga jam’iyyar APC. Usman ya bayyana rikicin cikin gida na jam’iyyar da rashin bin ka’idojin dimokuradiyya a matsayin dalilinsa na ficewa daga jam’iyyar. ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi Shiddi, wanda ya wakilci mazabarsa a majalisar wakilai ta 8 da ta 9, ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da manema labarai a ranar Lahadi. Tsohon dan majalisar ya ce, matakin da ya dauka na ficewa daga jam’iyya mai mulki ya biyo bayan tunani na tsawon watanni da kuma kara nuna damuwa game da abin da ya bayyana a matsayin ficewar jam’iyyar APC daga dabi’un da suka zaburar da shi tsunduma cikinta a baya. Sai dai kuma, tsohon dan majalisar bai bayyana matsayinsa na siyasa na gaba ba duk da cewa an kada gangar zaben 2027 inda ‘yan adawa ke barazanar hambarar da jam’iyyar APC mai mulki daga mulki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
  • “Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa
  • Iran tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Tsakanun Kasashen Yankin
  • Yunkurin Netanyahu na mamaye Gaza ya tayar da balli a Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • An Samu Bullar Sabani Da Rikici Tsakanin ‘Yan Sahayoniyya Game Da Batun Mamaye Zirin Gaza
  • FG Za Ta Raba Naira miliyan 3.4m Ga Wadanda Suke Amfana Da Shirin ACReSAL
  • Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
  • Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
  • Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli