HausaTv:
2025-11-08@21:08:59 GMT

“Amnesty International”: Korar Falasdinawa Daga Gaza Laifin Yaki Ne

Published: 7th, May 2025 GMT

A yau Laraba kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty Interantional” ta fitar da rahoto da a ciki ta yi kira ga HKI da ta kawo karshen shirinta na korar Falasdinawa daga Gaza da karfi, tare da cewa; Har yanzu Isra’ilan tana ci gaba da tafka laifukan yaki a Gaza da yi wa mutane kisan kiyashi.”

Haka nan kuma kungiyar kare hakkin bil’adaman ta kasa da kasa ta ce; Isra’ilan tana fakewa da batun fursunoni domin halartawa kanta aikata laifukan yaki akan Falasdinawa.

A wani rahoto na sirri da aka yi kwarmatonsa,an nuna yadda gwamnatin HKI ta amince da sake mamaye yankin zirin Gaza baki daya.

Tashar talabijin ta 12, ta ambata cewa Shirin wanda majalisar ministoci ta amince da shi, ya kunshi sake mamaye zirin  Gaza daga Arewacinsa zuwa kudancinsa.

A watan Febrairu ne dai shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi Magana akan Shirin fitar da Falasdinawa daga Gaza, da mayar da yankin zama wurin shakatawa.

A wancan lokacin dai kasashen duniya sun yi tir da furucin na Trump daga ciki har da kasashen turai abokan kawancen Amurka.

A halin yanzu dai HKI tana mamaye da kaso 1/3 na yankin Gaza, tare da rufe dukkanin kofofin shigar da tallafin abinci zuwa yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin November 8, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong November 8, 2025 Daga Birnin Sin Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE November 8, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin
  • CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin
  • Nigeria: Za A Ci Gaba Da Zaman Shari’ar Shugaban Kungiyar “IPOB” A ranar 20 Ga Watan Nan Na Nuwamba
  •  Lebanon: Mutane 2 Sun Jikkata Sanadiyyar Harin “Isra’ila” A Garin Bint-Jubail
  •  Tanzania: An Tuhumi Mutane Da Dama Da Laifin Cin Amanar Kasa Bayan Rikicin Zabe
  • Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza
  • Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta
  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan
  • Kwamitin Tsaron Ya Ce: Amurka Ta Bukaci Duba Kudurin Neman Kafa Rundunar Kasa Da Kasa A Gaza