HausaTv:
2025-06-23@02:00:40 GMT

 Hare-haren Hizbullah Sun Jazawa HKI A Fagen Gona Asarar Dala Miliyan 108

Published: 7th, May 2025 GMT

Wani rahoto na musamman da HKI ta gudanar akan asarar da ta fuskanta sanadiyyar yaki da Hizbullah, ya bayyana cewa, a fagen aikin gona kawai sun yi asarar dalar Amurka miliyan 108 wacce ta fara daga 8 ga watan Oktoba 2023.

Kungiyar ReGrow Israel” ta ce, yakin da aka yi da Hizbullah ya yi barna gagaruma a fagen aikin gona da asarar da ta kai ta dala miliyan 108 a kan iyaka da Lebanon.

Nazarin wannan kungiyar ya kuma kara da cewa; Tun daga ranar 8 ga watan Oktoba 2023 har zuwa lokacin tsagaita wutar yaki a karshen 2024, hare-haren Hizbullah sun lalata muhimmacin cibiyoyi a “Isra’ila” da kuma haddasa gobara mai girma, da hakan ya tilastawa mazaunan yankin, musamman manoma yin hijira.

Bugu da kari, binciken ya ce, barnar da yakin ya haddasa akan gonaki, ya haddasa koma baya a fagen samar da abinci, da kuma kawar da daidaito a kasuwanni.

Shugabar zartarwa ta kungiyar “ReGrow Isra’el” Danil Abraham,  ta sanar da cewa; Barnar da aka samu a kan iyaka da Lebanon tana da girman gaske, da kuma rikiritarwa, ta kuma shafi yanki mai girma fiye da fagen dagar Gaza.

Abraham ta kuma ce; Sai 9000 aka kai wa arewacin “HKI” hare-hare da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuki, da hakan ya sa gonaki masu yawa su ka kone. Haka nan kuma kaso 60% na manoman a Arewacin HKI, sun dakatar da ayyukansu baki daya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’

Fadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai zabi wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2027 a hukumance ne kawai bayan a kammala babban taron jam’iyyar APC a 2026.

Kakakin shugaban, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawarsa da jaridar Daily Trust a ranar Alhamis.

Da yake martani kan dalilin da ya sa fadar shugaban ta yi shiru kan zargin cewa Tinubu na son canza mataimaki a 2027 musamman la’akari da yadda ’yan jam’iyyar ke ta nuna goyon bayansu ga shugaban shi kadai, Onanuga ya ce hakan ba gaskiya ba ne.

Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — Birtaniya

A cewarsa, “Lokacin da na karanta labarin, na karyata shi saboda ba shi da tushe. A tsarin shugaba mai cikakken iko da Najeriya ke bi, dan takarar shugaban kasa ake fara zaba, shi kuma sai ya zabi wanda zai yi masa mataimaki. Abin da ya faru ke nan a lokacin Buhari – an fara zabensa, sai daga baya shi kuma ya dauki mataimaki. Ba a yin duka biyun a lokaci daya.

“Da zarar INEC ta fitar da jadawalin zabuka, jam’iyya za ta shirya babban taronta, idan aka sake tsayar da shugaban kasa, shi kuma zai zabi mataimakinsa,” in ji Onanuga.

Kazalika, ya kuma yi fatali da tarihin da ake daukowa cewa sau biyu tinubu yana canza mataimaka lokacin da ya yi Gwamna a jihar Legas daga 1999 zuwa 2007, cewa irin haka za ta faru da Kashim Shettima a 2027.

Ya kuma ce jita-jitar da ake yadawa a kan yiwuwar canza Shettima tun ma kafin a fara nuna amincewa da sake takarar Tinubu ba ta da tushe.

Ya ce, “Ba ni da masaniya a kan duk wani sabani tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa. Iya abin da na sani shi ne akwai kyakkyawar fahimtar juna da alakar aiki mai kyau a tsakaninsu. Duk maganganun da ake yadawa ba su da maraba da na teburin mai shayi. Mutane na ta fadara maganganun rashin kan gado cewa wai Seyi Tinubu ne ma mataimakin shugaban kasa. Wannan shashanci ne.

“A wannan kasar, mukamin mataimaka ko na gwamna ko na shugaban kasa ba a raba su da ’yan tsegungumin mutane. Ko da ana zaune lafiya babu wata matsala, makunsantansu sai sun kirkiri husuma da labaran karya. Amma iya abin da na sani shi ne babu matsala tsakanin Tinubu da Shettima.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi
  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — Abba
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
  • Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano
  • An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka
  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’