“Mun rufe dukkan sansanonin ‘yan gudun hijira da ke cikin Maiduguri. Yanzu haka saura biyu da ba na hukuma ba. Mun riga mun dawo da kashi 75 na ‘yan sansanin Muna gida, saura kashi 25 za su koma cikin kwanaki masu zuwa.”

Kowane iyali sun samu tallafin abinci, kayan gini da kulawar lafiya.

Haka kuma, kowane magidanci mace ko namiji za a ba shi Naira 100,000, yayin da matan gidan za su ƙara samun Naira 50,000 don taimaka musu da buƙatunsu na yau da kullum.

Za a Ƙara Inganta Cibiyar Koyo Sana’o’i a Gidan Gyaran Hali

Tun da safiyar ranar Litinin, Gwamna Zulum ya kai ziyara gidan gyaran hali na manyan laifuka da ke Maiduguri.

Ya ce za a inganta cibiyar koyar da sana’o’i da ke gidan don taimaka wa fursunoni su koyi sana’a da za su yi amfani da ita bayan an sake su.

“Manufar ɗaure mutum a gidan gyaran hali ita ce gyara halayensa, ba wai tsare shi kawai ba. Wannan ba zai yiwu ba sai akwai kayan aikin koyarwa da ake buƙata” in ji Zulum.

“Za mu duba wasu daga cikin fursunonin da ke da ƙananan laifuka, mu gani ko akwai yiwuwar a sake su bisa doka.”

Zulum ya samu rakiyar ɗan Majalisar Tarayya, Bukar Talba, shugaban ma’aikatansa na riƙon ƙwarya, mai ba shi kan harkokin addini da wasu jami’an gwamnati.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Gudun Hijira Boko Haram Hari

এছাড়াও পড়ুন:

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Kazalika, dalibai su kasance suna iya yin bayani a kan abin da suka fahimta na abin da aka koya musu, sannan su rika bayar da shawarwari, su kasance za su iya yin wani abu ta kirkira, su yi mu’amala da wasu ba tare da wata matsala ba, su ba da hadin kai, su kasance suna iya yin abin da ake so su yi.

Idan har aka samu damar magance wadannan matsaloli da aka ambata a sama tare kuma da tabbatar hanyoyin da ake bi koyarwa, ta haka za a iya samun gyaran da ake bukata. 

Bankin duniya a shekarar (2019) ya ce, ana fara samun sauyi ne daga Malaman makaranta; wadanda suka san abin da suke yi da kuma irin salon da ake amfani da shi wajen koyarwa. Bugu da kari kuma, ya kamata masana ilimi su yi amfani da irin ci gaban da fasaha ta kawo a wannan fanni na koyarwa.

Wasu Abubuwa Da Suka Shafi Ilimi A Duniya 

Kashi 88 na yara mata da kuma kashi 91 na yara maza, suna da ilimin Firamare, sai dai kuma mata da dama na samun ilimi mai zurfi fiye da maza, (World Economic Forum, 2019). 

A shekarar 2020, yawancin wadanda suka kammala karatun Firamare a fadin duniya baki-daya, kashi  90.14 cikin 100 ne, (UNESCO, 2021e). 

A cikin shekarar, an samu raguwar wadanda suka kammala karatun Sakandaren da kashi 77 cikin 100, (UNESCO, 2021d).

Haka nan ma, wadanda suka yi makarantar yaki da jahilci ‘yan shekara 15 da wadanda suka haura haka, kashi 86 ne cikin 100, (UNESCO, 2021c).

Wadanda suka yi yaki da jahilci ‘yan shekara 15 da wadanda suka haura haka, sun zarce kashi 83.3 cikin 100, yayin da su kuma maza suka kasance kashi 90 cikin 100, (UNESCO, 2021a; UNESCO, 2021b).

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
  • An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana
  • Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto
  • Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari
  • Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 
  • Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal
  • Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
  • Kar a kuskura a shiga cikin yaƙin Iran da Isra’ila — MDD
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama