HausaTv:
2025-08-05@08:13:02 GMT

AU, ta yi tir da harin baya bayan nan a tashar ruwan Sudan

Published: 6th, May 2025 GMT

Kungiyar Tarayyar Afrika (AU), ta yi tir da hari na baya-bayan nan da aka kai Port Sudan, muhimmin birni a kasar Sudan dake cikin ’yan kalilan da yakin da ake yi a kasar bai shafa ba.

Port Sudan ya taka muhimmiyar rawa a matsayin cibiyar jigila da ayyukan agaji, yayin da ake ci gaba da gwabza fada a Sudan.

Kungiyar AU mai mambobi 55 ta yi gargadin cewa, kai hari birnin zai kawo tsaiko ga kokarin da ake yi na wanzar da zaman lafiya a kasar.

Rahotanni daga kafafen yada labarai na cewa, kungiyar RSF ta kai hari da jirgi mara matuki zuwa filin jirgin sama na sojoji, da sauran wuraren dake filin jirgin sama na kasa da kasa na Port Sudan, a ranar Lahadi.

An ce harin shi ne irinsa na farko da RSF din ta kai Port Sudan

Kafafen watsa labaran cikin gida sun ba da rahoton kai hari tashar jiragen ruwa da wasu gine-ginen gwamnati.

An ji tare da ganin fashewar bama-bamai da wuta nan da can a birnin na Port Sudan, wanda wannan shi ne kwana na uku a jere da birnin ke shan ruwan bama-bamai da ake kai harin ta hanyar kananan jiragen sama marassa matuka, kamar yadda wasu kafofin watsa labarai na kasar ke bayyanawa.

Su ma makwabtan kasar ta Sudan, Masar da Saudiyya sun yi Alllwadarai da hare haren , ita ma majaliasar dinkin duniya ta nuna damuwa a kai.

Tun watan Afirilu na 2023 Sudan ta fada wannan mummuna yakin basasa tsakanin kungiyar ta RSF da kuma rundunar sojin kasar wadanda a da suke tare – rikici kann sabanin mayar da mulki tsarin farar hula ya raba kansu.

Rikicin ya raba mutum ,iliyan 12 da muhallinsu kuma ya jefa rabin yawan alummar kasar cikin matsananciyar yunwa, kamar yadda majalaisar dinkin duniya ta ce.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu

Kungiyar Hamas wacce takr iko da Gaza kuma take gwagwarmaya da HKI tun shekara ta 2023 a baya-bayan nan, ta bayyana cewa ba za ta ajiye makamanta ba sai an kafa kasar falasdinu mai zaman kanta, wanda yin watsi ne da bukatar HKI na shafe kungiyar daga doron kasa.

Shafin labarai na Internet Arab News na kasar Saudiya ya nakalto kungiyar tana fadar haka bayan da taron tattaunawa ta tsagaita budewa juna wuta na kwanaki 60 ya tashi baram-baram a birnin Doha na kasar Qatar.

Labarin ya kara da cewa, a ranar Talatan da ta gabata ce, kasashen Qatar da Masar suka amince da ra’ayin samar da kasashe biyu a kan kasar Falasdinu da aka mamaye, a matsayin hanya Tilo ta warware rikicin Falasdinawa da yahudawan HKI, sannan a lokacin ne Hamas zata mika makamanta ga gwamnatin jeka na yika ta Palasdinawa waccea take samun goyon bayan kasashen yamma da kasashen larabawa.

Amma kungiyar Hamas ta amsawa wadannan kasashe kan cewa kungiyar ba zata taba ajiye makamanta ba, sai bayan an kafa kasar Falasdinu mai cikekken yenci da kuma birnin Qudus a matsayin babban birnin Qasar.

HKI tana ganin duk wata yarjeniyar da za’a cimma da Hamas idan bai hada da karbe makamanta b aba abin amincewa ne gareta ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Hamas Ta Wallafa Hotunan bidiyo Na Fursinan HKI tsare A Gaza August 3, 2025 Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62 August 3, 2025 Pezeskkian Ya Ce: Suna Fatan Musayar Kasuwancin Tsakanin Iran Da Pakistan Ta Haura Dala Biliyan 10 August 2, 2025 Araqchi: Abokantaka Da Ke Tsakanin Iran Da Pakistan Wata babbar Jari Ce Nan Gaba August 2, 2025 Jaridar Isra’ila Ta Ce: Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Sha Kashi A Yakin Gaza   August 2, 2025 Dakarun Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 2, 2025 Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka August 2, 2025 Shugaba Pezeshkiyan Ya Yi Juyayin Shahadar Haniya Bayan Shekara Guda Da Shahada August 2, 2025 MDD: HKI Ta Kashe Falasdinawa Fiye Da 100 A Cikin Kwanaki 2 A Lokacinda Suka Karban Abinci August 2, 2025 Mutanen Kasar Siriya Sun Fito Zanga-Zanga Yin Allawadai Da Kissan Alawiyya A Kasar August 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
  • Za a samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya na kwanaki uku a faɗin Nijeriya — NiMet
  • Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura
  • Jerin gwanon nuna goyon baya ga al’ummar Gaza a Sydney Australia
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin  Shiri
  • Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu
  • Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
  • Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
  • Dakarun Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing