Aminiya:
2025-08-12@17:01:10 GMT

HOTUNA: Yadda aka baje kolin kayan laifin da ’yan sanda suka kama a Abuja

Published: 2nd, May 2025 GMT

Kalli ya da Kwamishinan ’Yan Sanda na Babban Birnin Tarayya, Ajao Saka Adewale, ya yi hole ababen hawa da sauran kayan laifi da rundunarsa ta kama a gaban ’yan jarida a ranar Juma’a.

Hotuna: Abubakar Sadiq Isah.

.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Kayan laifi

এছাড়াও পড়ুন:

Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila

Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ce ta karfafa matakan tsaro a yankin Babanla biyo bayan harin da wasu da ake zargin mahara ne suka kai musu, inda suka kashe mutane 5 ciki har da dan sanda Adejumo Wasiu.

 

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, SP Adetoun Ejinre-Adeyemi ya fitar, ya ce ‘yan fashi da makami da yawansu ya kai daruruwa, a kan babura, sun mamaye al’ummar Babanla a karamar hukumar Ifelodun.

 

A cewarsa wadanda ake zargin sun kai hari ne a hedikwatar ‘yan sanda inda suka kai farmaki cikin kasuwar.

 

Ya bayyana cewa maharan sun yi ta harbe-harbe kai-tsaye, inda suka kashe mutane 5 ciki har da dan sanda Adejumo Wasiu.

 

Sanarwar ta ce jami’an ‘yan sanda, jami’an Sojin Najeriya, ‘yan banga, da mafarauta cikin gaggawa sun dakile harin, tare da dawo da zaman lafiya, tare da fara farautar wadanda suka kai harin.

 

Ya yi nuni da cewa kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kwara, Adekimi Ojo, tare da rakiyar daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS), sun kai ziyarar tantancewa Babanla domin tantance yanayin tsaro.

 

Sanarwar ta ci gaba da cewa, an samar da wani babban tsari domin tabbatar da zaman lafiya da karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomi da tsaro a cikin al’ummar da lamarin ya shafa.

 

Ta ce tawagar jami’an tsaron hadin gwiwa sun zagaya muhimman wurare a cikin al’umma – ciki har da kasuwa, da hedikwatar ‘yan sanda, da kewaye domin tabbatar da cewa an samu kwanciyar hankali.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Kwastam ta kama makamai da ƙwayoyin N10bn a Legas
  • Babban Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Ce: ‘Yan Gwagwarmaya Sun San Abubuwan Da Suka Dace
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila
  • Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 
  • NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
  • Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu