Leadership News Hausa:
2025-06-17@18:21:59 GMT

Wutar Lantarki Ta Kashe Mutum 112, Wasu 108 Sun Jikkata A 2024

Published: 2nd, May 2025 GMT

Wutar Lantarki Ta Kashe Mutum 112, Wasu 108 Sun Jikkata A 2024

Haka zalika, mutuwar mutane 33 da jikkata 54 sun faru ne sakamakon munanan ayyuka na ganganci da rashin yanayi mai kyau, yayin da yin aiki ba bisa ka’ida ba ya kai ga mutuwar 23 da jikkata shida.

Masu barnatawa da lalata kayan wuta sun janyo mutuwar mutane 18 da jikkata wasu 7, sai kuma hatsarin fadowa daga sama ya janyo mutuwar mutum daya da jikkata wasu 18.

A Nijeriya dai sama da shekaru ana fama da matsalar rasa rayukansu da jikkata mutane da dama daga hadurran da suka shafi na wutar lantarki kuma wannan mafi akasari na faruwa ne sakamakon amfani da kayan wuta marasa inganci ko marasa kyau, karancin amfani da kayayyakin kariya, ayyukan masu lalata kayan wuta da kuma yin gina kusa ko a kasar layukan wutar lantarki da dai sauran matsalolin.

Da yake zantawa da manema labarai, Manajan Daraktan Hukumar Kula da Ayyukan Wutar Lantarki ta Nijeriya (NEMSA), Injiniya Aliyu Tahir, ya ce binciken da aka yi a kan dukkan hadurrukan da suka wakana ya zuwa yanzu ya nuna cewa da yawa daga cikinsu wadanda lamarin ya shafa sun hada da ma’aikatan kamfanonin samar da wutar lantarki.

Injiniya Tahir ya lura kan cewa hadurran mafi yawansu sun faru ne sakamakon rashin kin bin ka’idojin aiki da matakan kariya a yayin gudanar da aiki da aikin kula da lamuran wuta.

“Muna ganin yadda ma’aikata ke aiki kan layukan wutar lantarki ba tare da kayan aikin kariya na ma’aikata ba.

“Muna kuma ganin yadda wasu ke hanzari da gaggawa yayin aikin gyara wuta. Wannan fa wutar lantarki ne. Wutar lantarki na tattare da abubuwa masu hatsari sosai, wadannan hatsarin suna kuma shafan masu gudanar da aikin, don haka bin matakan kariya da kiyayewa da sanya kwarewa a bangaren aiki ne kawai zai kai ga rage matsalolin nan,” ya shaida.

Ya ce, hukumar tana kan sake nazarta matakan kariya domin tabbatar da kamfanonin wutar lantarki suna bi domin kare kai tare da sahalewa da amincewar NERC.

Alkalin-alkalan Nijeriya, Mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta yi kira ga bangaren shari’a da su tabbatar da daukar nauyin kamfanonin wutar lantarki da aka samu sakamakon mace-macen wutar lantarki a kasar nan.

Da take jawabi yayin wani taron kara wa juna sani da Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC) ta shirya a Abuja, ta bayyana fargaba kan mutuwar mutane 112 da suka samu wutar lantarki da kuma jikkata 95 a shekarar 2024 kadai.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: wutar lantarki Wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya soke ziyarar aiki da ya shirya zuwa Kaduna, a maimakon haka zai ziyarci Jihar Benuwe domin jajanta wa al’umma sakamakon kashe-kashen da aka samu a jihar a baya-bayan nan.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar a ranar Litinin.

Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe

Kakakin ya ce Shugaba Tinubu zai kai ziyarar ce a ranar Laraba domin duba halin da jihar ke ciki bayan kashe-kashen da aka samu a ’yan kwanakin nan a jihar.

Haka kuma, a yayin ziyarar, shugaba Tinubu zai gana da masu ruwa da tsaki da suka haɗa da sarakuan gargajiya da ’yan siyasa da jagororin addini da shugabannin al’umma da kungiyoyin matasa, da nufin lalubo hanyoyin magance rikicin jihar.

Tuni dai shugaban ya aike da tawagar wakilan Gwamnatin Tarayya a yau da ta ƙunshi Sakataren Gwamnatin Tarayya da Babban Sufeton ’yan sanda da shugabannin hukumomin tattara bayanan sirri ta ƙasa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro da shugabannin kwamitsocin tsaro a majalisun dokokin ƙasar.

Fadar shugaban kasar ta ce wata babbar tawagar manyan jami’an tsaron Nijeriya ta isa Jihar Benuwe domin bayar umarnin yadda za a tunkari matsalar rashin tsaron da jihar ke fuskanta da kuma mai do da kwanciyar hankali.

A ƙarshen mako ne dai aka samu munanan hare-haren da suka yi sanadin kashe fiye da mutum 100 a Jihar Benuwe.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran
  • Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda
  • Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe
  • Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan
  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe