Shugaban hukumar al-adun musulunci da sadarwa a nan Iran Mohammad Mehdi Imamipour ya bayyana cewa za’a gudanar da taron kasa da kasa na kare hakkin bil’adama a karon farko a nan kasar Iran tare da mahangar kasashen gabas.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Imanipour yana fadar haka a yau, ya kuma kara da cewa za’a bude tarurrukan ne a nan birnin Tehran, Qom da kuma Esfahan a lokaci guda daga ranar 28 ga watan Afrilu zuwa 2 ga watan mayu.

Labarin ya ce matsalar kare hakkin bil’adama yana daga cikin al-amuran da ake nuna faska biyu a cikin al-amura da dama a duniya, musamman kan abinda yake faruwa a kasar. Imanipour y ace suna son gudanar da taron ko wani shekaru 4.

Ya zuwa yanzu dai inji shi, an gayyaci masana da kwararru daga kasashe 32 a duniya. Sannan an karbi rubuce-rubuce har 491, daga ciki 186 daga Amurka, Austria, Masart, Kenya, Tunisia, Rasha, China, Kazakhstan, Indonesia, Lebanon, Malaysia, Iraq, Nigeria, Serbia, Espaniya da kuma Netherlands. Har’ila yau tare da 305 daga cikin gida.

Daga karshe yace JMI tana son a samarda wata sabuwar mahanga ta kare hakkin bil’ada a duniya sabanin wadanda kasashen yamma suke jagoranta a halin yanzu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran

Farashin Man Fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin da Isra’ila ta kai wa Iran, lamarin da ya tayar da hankalin masu zuba jari.

Ana fargabar cewa rikicin da ke ƙara taɓarɓarewa tsakanin ƙasashen biyu zai iya kawo tangarɗa wajen samar da man fetur daga yankin Gabas ta Tsakiya.

An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8

Wani muhimmin wurin da ake safarar man fetur na duniya, wato mashigar Hormuz da ke kusa da Iran na da matuƙar tasiri, domin kashi ɗaya cikin biyar na dukkanin man da ake fitarwa daga nan ne ake bi da shi.

Amma duk da haka, kasuwannin hannun jari sun fuskanci faɗuwar daraja saboda rashin tabbas da harin ya haifar.

Sai dai darajar wasu hajojin da ake ɗauka amintattu a lokutan rikicin irin su zinariya da kuɗin ƙasar Japan, Yen sun tashi sama, domin masu zuba jari na ƙoƙarin neman mafaka a cikinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Birgediya Pakphur: Nan Gaba Kadan Za A Budewa “Isra’ila” Kofofin Jahannama
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita