HausaTv:
2025-06-23@18:09:54 GMT

ECOWAS Zata YI Taro A Ghana Don Tattauna Batun Niger, Mali Da Burkina Faso

Published: 22nd, April 2025 GMT

Kungiyar raya tattalin arziki ta kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fara taro a kasar Ghana don tattauna al-amura da suka shafi kasashen Niger Burkina Faso da kuma Mali.

Jaridar Premium times ta Najeriya ta bayyana cewa agendar taron nasu na kwanaki biyu, sun hada da huldar kungiyar da kasashen uku, musamman cibiyoyin ECOWAS da suke cikin kasashen, sannan da batun kudaden fito na kashi 0.

5% wanda kungiyarsu ta (AES) ta dorawa kayakin da suke shigowa  kasashensu da sunan gudanar da kungiyarsu. Labarin yace kungiyar ECOWAS bata karban kudaden fito da Visa  daga kasashen kungiyar gaba daya tun kafin kasashen uku su fita amma a halin yanzu su suna karba. Kasashen uku sun bayyana ficewarsu daga ECOWAS ne daga farkon wannan shekarar.

Daga karshe kungiyar ta bayyana cewa zata fidda tsarin tattaunawa da kasashen uku daya bayan daya don warware matsalolin da ficewar daga kungiyar suka haddasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari wasu ƙauyuka biyu da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna.

A yayin harin, wata matar aure ta rasu, yayin da wani manomi ya samu rauni.

’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa  Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani

Harin farko ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na daren ranar Asabar, 21 ga watan Yuni, 2025, a ƙauyen Ungwan Sarkin Hausa da ke Rimau.

Ana zargin maharan sun gudu da shanun da suka sato daga Ƙaramar Hukumar Kauru.

A lokacin harin, sun kashe wata mata mai suna Misis Alheri Danzaria.

Sun kuma sace wasu mutum biyu, amma daga baya suka sake su.

Hari na biyu ya faru ne da safiyar ranar Lahadi da misalin ƙarfe 7 a ƙauyen Kallah.

A nan ne suka harbi wani manomi mai suna Mista Iliya Barde, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa gona.

An garzaya da shi asibiti inda yake samun kulawar likitoci.

Shugaban gundumar Kufana, Mista Stephen Maikori, ya ce hare-haren da ake yawan kai wa sun haddasa tsoro da damuwa a tsakanin mazauna yankin.

Ya buƙaci gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa wajen ƙara tsaro a yankin.

Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya ce zai bincika lamarin sannan ya bayar da amsa, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto bai yi ƙarin haske ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS
  • An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Batun Rushe Gidaje A Unguwar Rimin Zakara Ba Gaskiya Ba Ne – Alhaji Naziru 
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
  • An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato
  • Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya
  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje