Leadership News Hausa:
2025-06-14@22:28:24 GMT

Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa

Published: 22nd, April 2025 GMT

Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa

Kamfanoni da masana’antun America da dama sun dakatar da harkokinsu, dubban mutane sun rasa aikin yi. Don haka wannan mataki bai haifar da sakamakon da Mr. Trump ke bukata ba, musamman idan aka yi la’akari da yadda kasuwar hannayen jari ta shiga cikin rudani, gami da hali na rashin tabbas da manoman America suka samu kansu biyo bayan maida martani da China tayi na ramuwar gayya.

Domin kuwa sai da gwamnatin America ta kashe kimanin dala biliyan 30 wajen tallafawa manoman kasar kan asarar da suka tafka, biyo bayan harajin da China ta kakabawa wasu daga cikin amfanin gonar America da ake shigar da su China.

 

Sabo da haka a nan za mu iya bugun gaba mu ce “Kwalliya bata biya kudin sabulu ba” a kan matakin da shugaba Trump ya dauka na sanya haraji akan kayayyakin da ake shiga da su America daga China da sauran kasashen duniya.

 

Tabbas Mr. Trump ya fahimci babban kuskuren da ya tafka na daukar wannan mataki na rashin sanin ya kamata. Watakila yana jin kunyar ya fito ya fadawa duniya cewa ya janye wannan mataki, shi ya sanya ya fake da cewa ya jinkirta ci gaba da aiwatar da harajin har zuwa kwanaki 90, ko da yake ya ce ban da China. Babu makawa nan ba da jimawa ba shugaba Trump zai lashe aman da ya yi, musamman idan talakawan America suka gaza jimrewa matsatsin tattalin arziki sakamakon hauhawar farashin da rashin aikin yi da sakamakon wannan mataki da Trump ya dauka. (Lawal Mamuda)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: wannan mataki

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai

Aƙalla jihohi 11 na Najeriya sun kashe sama da Naira biliyan 6.2 wajen tallafa wa Alhazansu domin sauƙaƙa musu wajen zama a ƙasar Saudiyya yayin gudanar da aikin Hajjin 2025.

Wannan tallafi ya haɗa da kuɗi, jakunkunan tafiya, da kuma sayen raguna na hadaya domin sallar Layya.

Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APC

Gwamnatin Jihar Sakkwato ce ta fi kowa bayar da tallafi mafi yawa, inda Gwamna Ahmed Aliyu, ya bai wa kowane daga cikin alhazai 3,200 na jihar Riyal 1,000 (kimanin Naira 450,000).

A Kano kuwa, kowane alhaji daga cikin alhazai 3,345 sun samu kyautar Riyal 50.

Gwamnatin Jihar Legas ta bai wa kowane daga cikin alhazai 1,315 Riyal 180 (kimanin N74,870), yayin da Jihohin Jigawa da Kebbi suka bayar da mafi ƙarancin adadi.

Wani jami’in Gwamna Sanwo-Olu ya bayyana cewa: “Kowane Alhaji ya samu Riyal 180 a matsayin kyauta don sauƙaƙa rayuwarsu a lokacin aikin hajji.”

Jihar Borno ba ta bayar da kuɗi ba, amma ta biya kuɗin ragunan layya (hadaya) na Alhazan jihar guda 2,174.

Haka kuma, hukumomin Kano sun sanar da cewa kowane Alhaji zai samu babbar jakar tafiya domin dawowarsa gida cikin sauƙi.

Sai dai masana da malamai sun soki irin wannan kashe-kashen kuɗi da gwamnati ke yi, inda suka bayyana hakan a matsayin almubazzaranci da rashin fifita abin da ya fi muhimmanci.

Farfesa Yahaya Tanko, masani a harkokin siyasa, ya ce: “Wannan ba fifiko ba ne. Ya kamata gwamnoni su mayar da hankali kan matsalolin tsaro da talauci, ba tare da kashe kuɗi kan aikin hajji ba.”

Ya ƙara da cewa: “Al’umma na fama da sace-sace, manoma ba sa iya zuwa gonakinsu, amma gwamnoni na kashe miliyoyi kan aikin Hajji. Wannan ba daidai ba ne.”

Hakazalika, babban malamin addini, Sheikh Fuad Adeyemi, ya ce: “Kuɗaɗen da aka kashe a kan Hajji za a iya amfani da su wajen taimaka wa ‘ya’yan Alhazai su yi karatu. Wannan zai amfanar da iyalai da kuma al’umma gaba ɗaya.”

Mutane da dama a kafafen sada zumunta sun bayyana irin wannan kashe kuɗi a matsayin rashin adalci ga talakawa.

Wasu sun ce aikin Hajji ibada ce da ya kamata mutum ko al’umma su ɗauki nauyinta da kansu, ba gwamnati ba.

Yanzu haka ana ta kira ga gwamnoni da su dawo da hankali kan tsaro, kiwon lafiya, da ilimi domin hakan ne zai amfani mafi yawan jama’a, ba wasu ƙalilan da suka samu damar zuwa aikin Hajji kawai ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas
  • Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai