Kwanan baya, kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya shirya taron bita tare da wadanda ba ’yan jam’iyyar ba, dangane da yanayin tattalin arzikin kasar, da kuma ayyukan tattalin arziki da za a aiwatar a rabin shekarar bana ta biyu, domin sauraren ra’ayoyinsu.

Xi Jinping, babban sakataren jam’iyyar ne ya shugabanci taron tare da ba da muhimmin jawabi, inda ya ce, dole ne a zage damtse wajen gudanar da ayyukan tattalin arziki a rabin shekarar bana ta biyu, kuma a tabbatar da gudanar da ayyukan ba tare da tangarda ba, kana a aiwatar da cikakken sabon tunanin raya kasa daga dukkan fannoni, da gaggauta kafa tsarin raya kasa, da kiyaye aiwatar da manufofi ba tare da matsala ba, da inganta aiwatar da manufofi tare da yin hangen nesa da sanin ya kamata.

Shugaban na Sin ya ce, ya zama wajabi a mayar da muhimmanci ga samar da guraben aikin yi, da kwantar da hankulan kamfanoni, da tafiyar da harkokin kasuwanci, da samar da tabbaci game da hasashen da ake yi kan tattalin arziki, da karfafa sayayya, da dakatar da yin takara maras dacewa, da kawar da cikas a kasuwar gida, da rungumar wani sabon tsarin ci gaba mai “zagaye biyu”, wato wanda zai tanadi amfani da kasuwar gida a matsayin jigo, tare da barin kasuwannin gida da na waje su karfafi junansu, a kokarin cimma manufar raya tattalin arziki, da zamantakewar al’ummar kasar a bana, da samun nasarar kammala shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 14. (Tasallah Yuan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tattalin arziki

এছাড়াও পড়ুন:

Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa tun daga shekarar nan ta 2025 har zuwa 2026.

IMF ya bayyana sabon hasashen a watan Yulin da muke ciki wanda a ciki ya yi ƙiyasin samun ƙarin bunƙasar tattalin arzikin Nijeriya.

Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa

Asusun ya yi hasashen samun ƙarin bunƙasar tattalin arzikin Nijeriya da kashi 3.4 a 2025, ƙari a kan hasashen kashi 3.0 da ya yi a watan Afrilu.

Haka kuma, IMF ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai samun ƙarin bunƙasa da kashi 3.2 a 2026, saɓanin hasashen kashi 2.7 da ya yi a watan na Afrilu.

Sai dai duk da wannan, wani rahoto IMF ya fitar a watan Yunin bana, ya ce Nijeriya na mataki na 12 a cikin jerin kasashe mafiya talauci a fadin duniya.

IMF ya ce talauci na kara karuwa a cikin kasar da ta dauki shekaru biyu tana kokarin sauya fuskar tattalin arziki, amma kuma take dada fadawa cikin duhu na tattalin arziki.

A cikin kasashe 189 da aka gudanar da bincike a cikinsu, Nijeriyar na a mataki na 178, inda ta zarta kasashe irin su Yemen da Sudan ta Kudu da Kwango da Nijar da Sudan, wadanda kusan dukkaninsu ke fama da rigingimu a halin yanzu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa