HausaTv:
2025-08-11@06:10:35 GMT

Sharhi:  Kalankuwar  Kona Rayayyu Da Wuta A Gaza

Published: 20th, April 2025 GMT

Sojojin mamayar HKI sun fara aiwatar da wani sabon kisa ta hanyar amfani da sabon salo akan Falasdinawa. Kai kace tsawon watanni 18 da su ka dauka suna amfani da makamai mabanbanta wajen kashe mutanen Gaza, bai isha sun cimma manufofin da su ka Sanya a gaba.

Sabon salon kisa wanda  ya yi kama da “Kalankuwar Masu Cin naman mutum” bayan sun soya shi, shi ne abinda yake faruwa.

 Isra’ila ta kai hari da jirgin yakin maras matuki na kunar bakin wake akan sansanonin ‘yan hijira da su ka yi dandazo a wuri daya. Iyalan Abur-Rus ne wannan jirgin kunar bakin waken ya fada a kansu  ya kashe da dama daga cikinsu ta hanyar kona su da ransu. Mutane 20 ne su ka kone kurmus a cikin wadannan iyalan na Abu-Rus.

A daidai lokacin da daruruwan mazauna wannan sansanin ‘yan hijirar su ka taru domin su kashe wutar da harshenta ke toroko da tashi sama, jikin iyalan Rus yana ci gaba da konewa har su ka yi shahada ba tare da an iya ceto su ba.

Bayan da wuta ta lafa, sauran danginsu da su ka saura da su ka zo daga nesa, sun dauki sa’oi ba tare da sun iya tantance wane da wane ba.

Wannan salon kisa na kone Falasdinawa da ransu, bai tsaya a cikin iyalan Abur-Rus ba, Isra’ila ta sake aike wa da wani jirgin saman maras matuki na kunar bakin wake zuwa wani sansanin ‘yan hijirar.  Wannan karon a unguwar “Razana” dake Beit-Lahiya a Arewacin zirin Gaza. Shi ma jirgin kunar bakin waken ya fada kan hemar iyalai guda da su ka kunshi Uba, Uwa, da ‘ya’yansu 4 tare da kone su kurmus.

 Kafin akai abinda ya saura na gangar jikin shahidai zuwa asibitin “Indonesia” dake Arewacin Gaza, wani jirgin sama maras matuki na kunar bakin wake, ya fada akan hemar wasu iyalan a sansanin ‘yan hijira na Jabaliya. A wannan karon iyalan “Asliyyah’ ya fada wa, ya yi sanadiyyar shahadarsu, su 7 baki daya. Sun kuwa kunshi kananan yara 5 da mahaifansu.

Da gari ya waye, mutanen sansanin ‘yan hijira na Jabaliya sun tashi da wani kisan kiyashin  akan makarantar Ayyubiyyah, dake karkashin hukumar Agaji. Wani jirgin maras matuki na ‘yan mamaya ya kai harin kunar bakin wake akan  wannan makaranta a daya daga cikin dakuna, da ya yi sanadiyyar shahadar ‘yan hijira 6 da kuma jikkatar wasu gwammai.

 **

A daidai wannan lokacin da HKI take shan jinin Falasdinawa ta hanyar kona su a raye, jiragen yakinta suna kai wasu hare-haren  a gidan iyalan Najjar dake Jabaliya. An kuwa sami shahidai 3. Haka nan kuma sun kai wasu hare-haren  a wata gona a garin Khan-Yunus da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 2.

Su ma manyan bindigogin HKI suna ci gaba da kai nasu hare-haren babu kakkautawa a sassa daban-daban na Gaza,musamman a unguwanni da suke gabashin birnin Gaza, da su ka hada ‘ al-tuffah’ shjaiyyah, da Sha’af da Beit Hanun.

Bai zama abin mamaki ba da hukumar lafiya ta duniya ( W.H.O) ta siffata Gaza da cewa ta zama “babbar makabarta”. Ta kuma kara da cewa; “Isra’ila tana kai wa hemomin ‘yan hijira hare-hare cikin sani, da kuma manufa.” Haka nan kuma hukumar ta ce; “Babu wani wuri wanda yake da aminci a cikin fadin Gaza”.Sannan ta kara da cewa; An hana ta shigar da kayan agaji na magunguna da sauran kayan aiki na likitanci saboda tarnakin da Isra’ila ta gindaya. Ta kuma Karkare da cewa; “Rashin abinci mai gina jiki a Gaza ta kai koli.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kunar bakin wake maras matuki na Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Tel Aviv: Dubban yahudawa sun yi zanga-zangar adawa da yakin Gaza

Dubban mazauna birnin Tel Aviv ne suka taru a tsakiyar birnin a daren jiya Asabar, domin neman kawo karshen yakin Gaza, kwana guda bayan da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta sanar da shirin kara kai hare-hare da kuma mamaye birnin Gaza.

Masu zanga-zangar dai na dauke da allula da kuma hotunan wadanda ake tsare da su a Gaza, suna masu kira ga hukumomi da su ba da fifikon sakin su kan fadada ayyukan soji.

An kuma bayyana cewa hatta a cikin manyan jami’an soji na Isra’ila, babban hafsan hafsan hafsoshin sojin Isra’ila  Eyal Zamir ya yi yunkurin shawo kan majalisar ministoci kan cewa mamaye Gaza ba shi ne zabin da ya dace ba, da kuma tattauna babbar illar da hakan zai haifar ga tasirin soji da tattalin arziki a irin wannan hali, kamar dai yadda jaridar Isra’ila Hayom ta ruwaito.

Zamir ya kuma nuna damuwarsa kan yadda mamayar Gaza za ta shafi rayuwar fursunonin da ake tsare da su da kuma makomarsu.

Mai Magana da yawun sojin Isra’ila ya ce,  Zamir na bayar da shawarar a cimma matsaya, inda ya jaddada bukatar yin sassauci da kuma kara zage damtse wajen ganin an cimma yarjejeniya, ya kara da cewa rundunar sojin kasar ta nuna a shirye ta ke ta amince da duk wasu sharudda da suka hada da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da za ta iya kawo karshen yakin.

A halin da ake ciki, ofishin Netanyahu ya sanar da cewa “Isra’ila” za ta karbe ikon birnin Gaza, ya kara da cewa “mafi rinjayen ministocin majalisar zartaswa sun yi imanin cewa shirin da aka gabatar wa majalisar ministocin ba zai cimma nasarar fatattakar Hamas ba ko kuma mayar da mutanen da aka yi garkuwa da su ba.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Welayati: Makircin Amurka da Isra’ila na kwance damarar Hizbullah ba zai yi nasara ba August 10, 2025 Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu August 10, 2025 Venezuela: An dakile yunkurin kai wasu munanan hare-hare a cikin kasar August 10, 2025 Pezeshkiyan Ya Yabawa Yan Jarida A Ayyukansu A Yakin Kwanaki 12 August 9, 2025 Yansanda A Burtaniya Ta kama Mutane Fiye Da 200 Masu Goyon Bayan Falasdinawa August 9, 2025 Iran Ta Yi Maraba Da Sulhuntawa Tsakanin Armenia Da Azerbaijan August 9, 2025 Falasdinawa 11 Ne Suka Rasa Rayukansu Saboda Yunwa A Gaza August 9, 2025 Shugaban Kwango, Tshisekedi Ya Shigar Yan Tawaye A Gwamnatinsa August 9, 2025 Iran: ‘Yan Sahayoniyya Na Shirin Share Falasdinawa Daga Kan Doron Kasa August 9, 2025 Iran: Amurka Ta Sha Kaye Daga ‘Yan Gwagwarmayar Kasar Yemen August 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Israila Ta Kashe ‘Yan Jarida 4 A Wani Hari Da Ta Kai Kan Tantinsu A Gaza
  • Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
  • Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
  • Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi
  • Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan
  • Tel Aviv: Dubban yahudawa sun yi zanga-zangar adawa da yakin Gaza
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno
  • ’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe
  • Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu