HausaTv:
2025-04-30@19:00:40 GMT

Sharhi:  Kalankuwar  Kona Rayayyu Da Wuta A Gaza

Published: 20th, April 2025 GMT

Sojojin mamayar HKI sun fara aiwatar da wani sabon kisa ta hanyar amfani da sabon salo akan Falasdinawa. Kai kace tsawon watanni 18 da su ka dauka suna amfani da makamai mabanbanta wajen kashe mutanen Gaza, bai isha sun cimma manufofin da su ka Sanya a gaba.

Sabon salon kisa wanda  ya yi kama da “Kalankuwar Masu Cin naman mutum” bayan sun soya shi, shi ne abinda yake faruwa.

 Isra’ila ta kai hari da jirgin yakin maras matuki na kunar bakin wake akan sansanonin ‘yan hijira da su ka yi dandazo a wuri daya. Iyalan Abur-Rus ne wannan jirgin kunar bakin waken ya fada a kansu  ya kashe da dama daga cikinsu ta hanyar kona su da ransu. Mutane 20 ne su ka kone kurmus a cikin wadannan iyalan na Abu-Rus.

A daidai lokacin da daruruwan mazauna wannan sansanin ‘yan hijirar su ka taru domin su kashe wutar da harshenta ke toroko da tashi sama, jikin iyalan Rus yana ci gaba da konewa har su ka yi shahada ba tare da an iya ceto su ba.

Bayan da wuta ta lafa, sauran danginsu da su ka saura da su ka zo daga nesa, sun dauki sa’oi ba tare da sun iya tantance wane da wane ba.

Wannan salon kisa na kone Falasdinawa da ransu, bai tsaya a cikin iyalan Abur-Rus ba, Isra’ila ta sake aike wa da wani jirgin saman maras matuki na kunar bakin wake zuwa wani sansanin ‘yan hijirar.  Wannan karon a unguwar “Razana” dake Beit-Lahiya a Arewacin zirin Gaza. Shi ma jirgin kunar bakin waken ya fada kan hemar iyalai guda da su ka kunshi Uba, Uwa, da ‘ya’yansu 4 tare da kone su kurmus.

 Kafin akai abinda ya saura na gangar jikin shahidai zuwa asibitin “Indonesia” dake Arewacin Gaza, wani jirgin sama maras matuki na kunar bakin wake, ya fada akan hemar wasu iyalan a sansanin ‘yan hijira na Jabaliya. A wannan karon iyalan “Asliyyah’ ya fada wa, ya yi sanadiyyar shahadarsu, su 7 baki daya. Sun kuwa kunshi kananan yara 5 da mahaifansu.

Da gari ya waye, mutanen sansanin ‘yan hijira na Jabaliya sun tashi da wani kisan kiyashin  akan makarantar Ayyubiyyah, dake karkashin hukumar Agaji. Wani jirgin maras matuki na ‘yan mamaya ya kai harin kunar bakin wake akan  wannan makaranta a daya daga cikin dakuna, da ya yi sanadiyyar shahadar ‘yan hijira 6 da kuma jikkatar wasu gwammai.

 **

A daidai wannan lokacin da HKI take shan jinin Falasdinawa ta hanyar kona su a raye, jiragen yakinta suna kai wasu hare-haren  a gidan iyalan Najjar dake Jabaliya. An kuwa sami shahidai 3. Haka nan kuma sun kai wasu hare-haren  a wata gona a garin Khan-Yunus da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 2.

Su ma manyan bindigogin HKI suna ci gaba da kai nasu hare-haren babu kakkautawa a sassa daban-daban na Gaza,musamman a unguwanni da suke gabashin birnin Gaza, da su ka hada ‘ al-tuffah’ shjaiyyah, da Sha’af da Beit Hanun.

Bai zama abin mamaki ba da hukumar lafiya ta duniya ( W.H.O) ta siffata Gaza da cewa ta zama “babbar makabarta”. Ta kuma kara da cewa; “Isra’ila tana kai wa hemomin ‘yan hijira hare-hare cikin sani, da kuma manufa.” Haka nan kuma hukumar ta ce; “Babu wani wuri wanda yake da aminci a cikin fadin Gaza”.Sannan ta kara da cewa; An hana ta shigar da kayan agaji na magunguna da sauran kayan aiki na likitanci saboda tarnakin da Isra’ila ta gindaya. Ta kuma Karkare da cewa; “Rashin abinci mai gina jiki a Gaza ta kai koli.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kunar bakin wake maras matuki na Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa

Wata koutun soja ta yanke wa wani jami’inta hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samun sa da laifn kashe buduwarsa.

Kotun da ta zauna a Hedikwatar Runduna ta 82 da ke Enugu, ta yanke wa Private Adamu Mohammed hukuncin kisa kan laifin budurwar taas mai suna Hauwa Ali.

Da yake sanar da hukuncin, Shugaban kotun, Birgediya Sadisu Buhari, ya ce, “Kotun Soja ta Kasa ta yanke hukuncin cewa sojan da ake tuhuma, mai lamba 21NA/80/6365 Private Adamu Mohammed, an yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa tuhumar kisan kai.”

Mukaddashin kakakin Rundunar, Jonah Unuakhalu, ya ce kwamitin kotun  ya cimma matsaya ɗaya bayan nazari mai zurfi na shaidu, tarihin aikin wanda ake tuhuma, da kuma roƙon sassauci daga lauyansa.

Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno

Ya shaida wa manema labarai a Abuja cewa kotun sojan, ta kuma yanke wa wani Soja mai suna Private Abubakar Yusuf hukuncin ɗaurin shekaru 10 a kurkuku saboda samun sa da laifin fashi da makami a wani shahararren kantin sayayya a Enugu.

Ya kara da cewa an yanke wa waɗannan mutane biyu hukuncin ne bayan kammala shari’o’insu kan laifukan kisan kai da fashi da makami.

Babban Kwamandan Runduna ta 82, Manjo-Janar Oluyemi Olatoye, ne ya kaddamar da kotun sojin a ranar 18 ga Fabrairu, 2025, domin yanke hukunci kan shari’o’in da suka shafi ma’aikatan da suka yi kuskure a cikin Rundunar.

A cewarsa, waɗannan hukunce-hukuncen sai sun samu tabbatarwa daga hukumomin soji da suka dace, wanda ya nuna ƙarshen shari’o’in sojojin.

Ya sake jaddada ƙudurin Sojojin Najeriya na tabbatar da ɗa’a da kuma kiyaye mafi girman ƙa’idoji na ɗabi’u da ƙwarewa.

“Kuskuren ayyukan wasu kaɗan ba su nuna ƙimar ƙungiyar ba. A koyaushe ana ɗaukar matakai masu sauri da kuma ƙarfi don tabbatar da riƙon amana da adalci,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine