Rundunar sojin sama na Operation Hadin Kai ta yi nasarar aiwatar da wasu hare-hare ta sama guda biyu, inda ta auka wa maboyar ‘yan ta’adda a yankin Sambisa na jihar Borno da kuma Kudancin Tumbun.

 

A wata sanarwa da Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na NAF, Air Commodore Ehimen Ejodame ya fitar, ya ce harin farko ya afku ne da misalin karfe 5:30 na safe a Kollaram- sanannar tungar ‘yan tada kayar baya, a ranar 15 ga watan Afrilu, inda aka kawar da mayaka da dama tare da lalata muhimman ababen more rayuwarsu.

 

Farmaki na biyu kuwa ya biyo bayan da misalin karfe 3:55 na rana a garin Arra na Sambisa, bayan binciken sirri da bincike da aka gudanar a baya an gano tarin ‘yan ta’addan, kuma hotunan da aka gani a zahiri sun tabbatar da kasancewar su. An yi amfani da ingantattun alburusai, wanda ya haifar gagarumar nasara da kuma kawo cikas ga ayyukan kungiyar.

 

A cewar sanarwar, wadannan ayyuka na baya-bayan nan wani bangare ne na ci gaba da yakin da aka tsara domin lalata karfin ‘yan ta’adda, da ruguza tsarin shugabancinsu da kuma kawar da mafakarsu a fadin Nijeriya.

 

PR/Usman Sani.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: barno Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

‘Yan bindiga sun sace ɗan majalisar dokokin Jihar Filato, mai wakiltar Pankshin Kudu, Laven Denty, a gidansa da ke unguwar Dong na ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.

A makon da ya gabata ma, Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito yadda ‘yan bindiga suka kutsa cikin unguwar Dong, inda suka yi garkuwa da wani mai yi wa ƙasa hidima (NYSC), da kuma ɗalibin Jami’ar Jos.

Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Ɓullar Cutar Mpox A Jihar Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

Masu garkuwar da mutanen sun shiga gidan iyalan Solomon Dansura, da misalin ƙarfe 10 na dare inda suka tafi da baƙinsa guda biyu a lokacin.

Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto babu wani martani daga hukumomin jihar ko kuma tabbaci daga rundunar ‘yansandan jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu, sun sace mutum 8 a Kwara
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Kama Masu Laifi
  • An Yanke Wa Sojojin Da Suka Sayar Wa ‘Yan Ta’adda Makamai Hukuncin Ɗaurin Rai-da-rai A Borno
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno
  • ‘Yan Gwagwarmaya  Sun Kashe Sojojin Mamaya Biyu A Wani Kwanton Bauna A Arewacin Gaza
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
  • Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina
  • An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike