Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun
Published: 18th, April 2025 GMT
Rundunar sojin sama na Operation Hadin Kai ta yi nasarar aiwatar da wasu hare-hare ta sama guda biyu, inda ta auka wa maboyar ‘yan ta’adda a yankin Sambisa na jihar Borno da kuma Kudancin Tumbun.
A wata sanarwa da Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na NAF, Air Commodore Ehimen Ejodame ya fitar, ya ce harin farko ya afku ne da misalin karfe 5:30 na safe a Kollaram- sanannar tungar ‘yan tada kayar baya, a ranar 15 ga watan Afrilu, inda aka kawar da mayaka da dama tare da lalata muhimman ababen more rayuwarsu.
Farmaki na biyu kuwa ya biyo bayan da misalin karfe 3:55 na rana a garin Arra na Sambisa, bayan binciken sirri da bincike da aka gudanar a baya an gano tarin ‘yan ta’addan, kuma hotunan da aka gani a zahiri sun tabbatar da kasancewar su. An yi amfani da ingantattun alburusai, wanda ya haifar gagarumar nasara da kuma kawo cikas ga ayyukan kungiyar.
A cewar sanarwar, wadannan ayyuka na baya-bayan nan wani bangare ne na ci gaba da yakin da aka tsara domin lalata karfin ‘yan ta’adda, da ruguza tsarin shugabancinsu da kuma kawar da mafakarsu a fadin Nijeriya.
PR/Usman Sani.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’
Fadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai zabi wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2027 a hukumance ne kawai bayan a kammala babban taron jam’iyyar APC a 2026.
Kakakin shugaban, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawarsa da jaridar Daily Trust a ranar Alhamis.
Da yake martani kan dalilin da ya sa fadar shugaban ta yi shiru kan zargin cewa Tinubu na son canza mataimaki a 2027 musamman la’akari da yadda ’yan jam’iyyar ke ta nuna goyon bayansu ga shugaban shi kadai, Onanuga ya ce hakan ba gaskiya ba ne.
Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — BirtaniyaA cewarsa, “Lokacin da na karanta labarin, na karyata shi saboda ba shi da tushe. A tsarin shugaba mai cikakken iko da Najeriya ke bi, dan takarar shugaban kasa ake fara zaba, shi kuma sai ya zabi wanda zai yi masa mataimaki. Abin da ya faru ke nan a lokacin Buhari – an fara zabensa, sai daga baya shi kuma ya dauki mataimaki. Ba a yin duka biyun a lokaci daya.
“Da zarar INEC ta fitar da jadawalin zabuka, jam’iyya za ta shirya babban taronta, idan aka sake tsayar da shugaban kasa, shi kuma zai zabi mataimakinsa,” in ji Onanuga.
Kazalika, ya kuma yi fatali da tarihin da ake daukowa cewa sau biyu tinubu yana canza mataimaka lokacin da ya yi Gwamna a jihar Legas daga 1999 zuwa 2007, cewa irin haka za ta faru da Kashim Shettima a 2027.
Ya kuma ce jita-jitar da ake yadawa a kan yiwuwar canza Shettima tun ma kafin a fara nuna amincewa da sake takarar Tinubu ba ta da tushe.
Ya ce, “Ba ni da masaniya a kan duk wani sabani tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa. Iya abin da na sani shi ne akwai kyakkyawar fahimtar juna da alakar aiki mai kyau a tsakaninsu. Duk maganganun da ake yadawa ba su da maraba da na teburin mai shayi. Mutane na ta fadara maganganun rashin kan gado cewa wai Seyi Tinubu ne ma mataimakin shugaban kasa. Wannan shashanci ne.
“A wannan kasar, mukamin mataimaka ko na gwamna ko na shugaban kasa ba a raba su da ’yan tsegungumin mutane. Ko da ana zaune lafiya babu wata matsala, makunsantansu sai sun kirkiri husuma da labaran karya. Amma iya abin da na sani shi ne babu matsala tsakanin Tinubu da Shettima.