Gwamnatin Yobe ta sayo hatsi don tunkarar kakar bana
Published: 18th, April 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Yobe ƙarƙashin jagorancin Gwamna Mai Mala Buni ta sayo ton 2,000 na hatsi iri-iri domin ƙarfafa samar da abinci da kuma tabbatar da shirin tunkarar kakar bana a matsayin gudun ko ta kwana.
A cikin wata sanarwa da Yusuf Ali, mai bada shawara ta musamman kan harkokin dabarun sadarwa na zamani (SSA) ga gwamna Buni ya ce, Kwamishinan ma’aikatar noma da albarkatun ƙasa, Ali Mustapha Goniri, ya kai ziyarar duba irin hatsin a shagunan bunƙasa noma na jiha da ke kan titin Gujba da ke Damaturu.
Da yake zantawa da manema labarai a yayin ziyarar, Ali Mustapha ya bayyana kyakkyawan fata game da shirin, inda ya jaddada cewa za a raba hatsin ga jama’ar Yobe a cikin gaggawa ko kuma lokacin bazara domin rage matsalar ƙarancin abinci.
Baya ga hatsin, Kwamishinan ya bayyana cewa gwamnati ta sayo nau’o’in sinadarai iri-iri domin tallafa wa manoman rani da kayan lambu.
Ya kuma bayyana shirin raba irin rogo ga manoma a fadin jihar, da nufin farfaɗo da noman na rogo lura da amfanin da ake yi da ita ta fuskoki iri-iri na abinci har ma da sarrafa ta da ake yi ya zuwa garin fulawa don yin abubuwa da ita.
Kwamishinan ya yabawa gwamnatin Gwamna Mai Mala Buni, bisa jajircewa da goyon baya da take bayarwa wajen bunƙasa harkar noma a Jihar Yobe.
Tawagar binciken ta haɗa da babban sakataren ma’aikatar, Barista Muhammed Inuwa Gulani da daraktoci da sauran jami’an ma’aikatar.
Wannan shiri ya ƙara jaddada ƙudirin gwamnatin Jihar Yobe na inganta samar da abinci da kuma baiwa manoma damar bunƙasa harkokin su na noma da nufin samar da ishasshen abinci a faɗin jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Mai Mala Buni
এছাড়াও পড়ুন:
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Ya ƙara da cewa ‘yan’uwa da abokan arziƙi da suka shirya wannan biki na karrama Farfesa Armaya’u Bichi tare da bashi lambar yabo tare da wasu muhimman mutane waɗanda suka taimaimake shi wajen gudanar da shugabanci sun kyauta sannan sun ajiye ƙwarya a gurbinta.
Shima da yake gabatar da jawabinsa, shugaban riƙo na jami’ar gwamnatin Tarayya dake Katsina (FUDMA), Farfesa Aminu Ado ya ce Bichi mutum ne mai jin tausayin al’umma musamman mutanen dake ƙarƙashinsa.
Farfesa Ado ya ce har ƙasa ta naɗe ba zai mance da irin gagarumin ci gaban da Farfesa Arma’yau ya kawo ma jami’ar FUDMA ba.
Haka kuma a yayin bikin an ƙaddamar da littafin waƙoƙin da wasu mawaƙa suka yi wa tsohon shugaban na FUDMA mai suna ‘MALAMI A BAKIN MAWAƘA,’ wanda wasu ma’aikatan jami’ar suka rubuta.
Babban mai ƙaddamar da littafin, kuma shugaban ƙungiyar Jami’oin Afrika masu zaman kansu, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo wanda ya samu wakilcin Dakta Ali Yusuf Kakaki ya sa ya sayi kwafi biyu a kan naira miliyan biyu (N2, 000, 000), sai kuma Sanata Alu Magatakardan Wamako ya sayi kwafi uku kan naira miliyan ɗaya.
Frafesa Armaya’u Bichi, ya nuna godiyarsa ga waɗanda suka shirya wannan taron domin taya shi murnar kammala aiki lafiya. Tare da jinjina da fatan alheri ga kafatanin waɗanda suka samu damar halartar wannan taro.
A yayin taron An karrama Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da shi kansa Farfesa Armaya’u Bichi da Farfesa Abubakar Rasheed da Malam Rufa’i Bichi da Malam Adamu Adamu, tsohon ministan ilimi a zamanin mulkin Buhari.
ranar Asabar 13 ga watan Satumban 2025 makusantan tsohon shugaban jami’ar Gwamnatin Tarayya dake Dutsinma ta jihar Katsina, Farfesa Armaya’u Hamisu Bichi sun gudanar da gagarumin taron murna da farin cikin kammala aiki lafiya tare da karrama shugaban rukunin jami’oin Maryam Abacha American University, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da lamar yabo.
Gagarumin bikin wanda aka gudanar da shi a babban ɗakin taro na kwalejin ilimi na Tarayya (FCE) Bichi ya samu halartar ɗimbin masoya daga ko’ina a faɗin Nijeriya.
Farfesa Abubakar Adamu Rasheed tsohon shugaban Hukumar dake kula da jami’oin ƙasa (NUC), a yayin da yake jawabi ya bayyana Farfesa Armaya’u a matsayin mutumin kirki mai tausayi da ƙaunar jama’a.
Ya ƙara da cewa ‘yan’uwa da abokan arziƙi da suka shirya wannan biki na karrama Farfesa Armaya’u Bichi tare da bashi lambar yabo tare da wasu muhimman mutane waɗanda suka taimaimake shi wajen gudanar da shugabanci sun kyauta sannan sun ajiye ƙwarya a gurbinta.
Shima da yake gabatar da jawabinsa, shugaban riƙo na jami’ar gwamnatin Tarayya dake Katsina (FUDMA), Farfesa Aminu Ado ya ce Bichi mutum ne mai jin tausayin al’umma musamman mutanen dake ƙarƙashinsa.
Farfesa Ado ya ce har ƙasa ta naɗe ba zai mance da irin gagarumin ci gaban da Farfesa Arma’yau ya kawo ma jami’ar FUDMA ba.
Haka kuma a yayin bikin an ƙaddamar da littafin waƙoƙin da wasu mawaƙa suka yi wa tsohon shugaban na FUDMA mai suna ‘MALAMI A BAKIN MAWAƘA,’ wanda wasu ma’aikatan jami’ar suka rubuta.
Babban mai ƙaddamar da littafin, kuma shugaban ƙungiyar Jami’oin Afrika masu zaman kansu, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo wanda ya samu wakilcin Dakta Ali Yusuf Kakaki ya sa ya sayi kwafi biyu a kan naira miliyan biyu (N2, 000, 000), sai kuma Sanata Alu Magatakardan Wamako ya sayi kwafi uku kan naira miliyan ɗaya.
Frafesa Armaya’u Bichi, ya nuna godiyarsa ga waɗanda suka shirya wannan taron domin taya shi murnar kammala aiki lafiya. Tare da jinjina da fatan alheri ga kafatanin waɗanda suka samu damar halartar wannan taro.
A yayin taron An karrama Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da shi kansa Farfesa Armaya’u Bichi da Farfesa Abubakar Rasheed da Malam Rufa’i Bichi da Malam Adamu Adamu, tsohon ministan ilimi a zamanin mulkin Buhari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp